Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Date:

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka karar da aka shigar game da mayar da Al-Mustapha Jokolo a matsayin Sarkin Gwandu har zuwa ranar 6 ga Yuni.

Kwamitin alkalai biyar karkashin jagorancin Mai Shari’a Uwani Abba-Aji ne ya sanya ranar a ranar Talata bayan da bangarorin da abin ya shafa suka gabatar da takardar hujjoji a kotu.

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

Kwamitin Alkalan ya kuma sanar da cewa duka daukaka kara guda hudu za su bi hukuncin da za a yanke kan daya daga cikin karar.

20250228 181700

A baya, lauyan gwamnatin Jihar Kebbi, Yakubu Maikyau (SAN), ya nemi izinin kotu domin gabatar da karin hujjoji a daukaka karar sa da aka shigar a ranar 19 ga Maris, 2025, kan hukuncin Kotun Daukaka Kara da aka yanke a ranar 14 ga Afrilu, 2016.

Haka kuma, ya jaddada cewa Babbar Kotun Jihar Kebbi ba ta da hurumin sauraron karar da Jokolo ya shigar a ranar 11 ga Disamba, 2014, don haka shari’ar da Kotun Daukaka Kara ta yi ba ta da inganci kuma ba ta da wani tasiri a doka.

Sai dai lauyan Jokolo, Sylvester Imhanobe Esq, ya bukaci kotu da ta yi watsi da karar tare da hukunta Gwamnan Jihar Kebbi, Antoni Janar na Jihar Kebbi, Alhaji Abdullahi Umar, da sauransu da biyan kudaden da suka dace, bisa gazawar su wajen gabatar da hujjojin da za su rushe hukuncin kotunan kasa da suka tabbatar da cewa gwamnan jihar bai gudanar da binciken da ya dace kamar yadda Sashe na 6 na Dokar Sarakuna (Nadin Sarauta da Tsige Sarauta) ta Jihar Kebbi ta tanada kafin tsige Jokolo ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...