Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP Ibrahim Adamu Bakori a matsayin sabon kwamishinan ƴansandan jihar Kano, inda zai maye gurbin CP Salman Garba Dogo wanda ya samu ƙarin girma zuwa mataimakin sifeto janar na ƙasa (AIG).
Kafiin naɗin nasa, CP Bakori ya kasance kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen binciken kisan jama’a a hedikwatar ƴansandan ƙasar da ke Abuja.
Yadda falakin Shinkafi ya sha ruwa da raba kayan sallah ga marayun da yake kula da su a Kano
Shugaban hukumar ƴansandan, DIG Hashimu Argungu mai ritaya ya nemi sabon kwamishinan na Kano da ya tabbatar an samu zaman lafiya mai ɗorewa a jihar.

Ya ƙara da cewa ya yi ƙoƙarin wajen tunkarar ƙalubalen da ke gabansa wajen tabbatar da an daƙile ƙaruwar aikata laifuka a jihar mai yawan jama’a.
Jihar Kano dai na fama da matsalolin dabanci da ƙwacen waya da sace-sace da kuma a baya-bayan nan rikicin masarautar Kano da ya janyo al’umma suka sauya tunaninsu kan rundunar ƴansandan jihar.