Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

Date:

 

 

Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP Ibrahim Adamu Bakori a matsayin sabon kwamishinan ƴansandan jihar Kano, inda zai maye gurbin CP Salman Garba Dogo wanda ya samu ƙarin girma zuwa mataimakin sifeto janar na ƙasa (AIG).

Kafiin naɗin nasa, CP Bakori ya kasance kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen binciken kisan jama’a a hedikwatar ƴansandan ƙasar da ke Abuja.

Yadda falakin Shinkafi ya sha ruwa da raba kayan sallah ga marayun da yake kula da su a Kano

Shugaban hukumar ƴansandan, DIG Hashimu Argungu mai ritaya ya nemi sabon kwamishinan na Kano da ya tabbatar an samu zaman lafiya mai ɗorewa a jihar.

InShot 20250309 102403344
Talla

Ya ƙara da cewa ya yi ƙoƙarin wajen tunkarar ƙalubalen da ke gabansa wajen tabbatar da an daƙile ƙaruwar aikata laifuka a jihar mai yawan jama’a.

Jihar Kano dai na fama da matsalolin dabanci da ƙwacen waya da sace-sace da kuma a baya-bayan nan rikicin masarautar Kano da ya janyo al’umma suka sauya tunaninsu kan rundunar ƴansandan jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...

Yadda falakin Shinkafi ya sha ruwa da raba kayan sallah ga marayun da yake kula da su a Kano

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa     Falakin Shinkafi Amb Yunusa Yusuf Hamza,...