Ta tabbata: NNPC ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Kamfanin mai na kasa NNPC ya sake rage farashin man fetur a Nigeria.

A baya dai ana sayar da man fetur din ne a gidajen man NNPC akan N965 amma yanzu farashin ya koma N860 kowacce lita.

Sai dai har yanzu kamfanin NNPC bai sanar da ragin a hukumance ba , amma dai majiyar kadaura24 ta Punch ta tabbatar da cewa an rage farashin a wasu gidajen mai dake jihar Lagos.

Duk Kokarin da majiyar ta mu ta yi na jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na kamfanin ya ci tura.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sai dai mataimakin shugaban kungiyar dillalan man fetur na kasa Hammed Fashola ya tabbatar da rage farashin man na kamfanin NNPC.

Shugaba Tinubu ya naɗa sabon shugaban NYSC

” Gaskiya ne NNPC ta fara sayar da mai akan N860 a gidajen mai, duk da cewar har yanzu ba su sanar da jama’a na, amma dai ni sun kirawo ni sun kuma fada min cewa za su yi wasu yan sauye-sauye.

20250228 181700

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta a makon da ya gabata ne matatar man Dangote ta rage farashin man na kamfanin zuwa N845 kowacce lita.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...