Ramadan: Sanata Barau ya bayar da tallafin kudi ga kungiyar Barau FC

Date:

 

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya bayar da kyautar tallafin kudi ga yan wasa, masu horarwa, da shugabannin kungiyar kwallon kafa ta Barau FC.

Rabon tallafin kudin na zuwa ne, ya yin da ake shirin shiga azumin watan Ramadan, da Sanata Barau ya bayar da tallafin kudin domin karfafawa yan wasan kungiyar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na kungiyar Ahmad Hamisu Gwale ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanata Barau, wanda ya sami wakilcin Kabiru Ado Lakwaya, mai taimaka masa kan harkokin matasa da wasanni, ya bayar da kyautar kudin ne a lokacin da ya ziyarci filin daukar horo na Kungiyar a ranar Juma’a a nan Kano.

Da dumi-dumi: Kotun Koli Ta Rushe Zaben Kananan Hukumomin Ribas

Kabiru Lakwaya ya ce wannan na daga cikin kokarin Sanata Barau Jibrin, na bayar da goyan baya ga yan wasa, da jamian kungiyar ta Barau FC.

A lokacin bayar da kyautar tallafin kudin, Kabiru Ado Lakwaya na tare da shugaban Barau FC Ibrahim Shitu Chanji, da Alhaji Abdul AP da Yahya Muhd da sauran masu ruwa da tsaki a kungiyar ta Barau FC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...