Gwamnan Kano ya haramta sanya dalibai aikin wahala a makarantu

Date:

Gwamnan jihar Kano Eng. Abba Kabir Yusuf ya gargadi malamai da su daina tilastawa dalibai yin aikace-aikace masu wahala a ciki ko a wajen makaranta

Haramcin na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sunusi Bature Dawakin-Tofa, ya aikowa Kadaura24 .

Gwamnan ya jaddada cewa makarantu wuraren karatu ne na koyar da ilimi da tarbiyya, ba wuraren yin aikin wahala ba.

InShot 20250115 195118875
Talla

Yayin wata ziyarar bazata da ya ka makarantar koyon harshen larabci (School for Arabic Studies) Kano, gwamnan ya tarar da wasu dalibai suna tonon ramin bututun bayan gida.

Inda cikin fushi, gwamnan ya tambayi shugaban makarantar dalilin da ya sa aka ba dalibai irin wannan aiki.

Shugaban makarantar ya shaidawa gwamna cewa aikin an ba su ne bayan an tashi daga makaranta.

Zargin batanci: Kotu ta aikewa Abdullahi Abbas da Faizu Alfindiki sammaci

Sai dai nan take gwamnan ya bayar da umarnin dakatar da yaran da aka sa aikin, ya kuma tabbatar wa shugabannin makarantar cewa gwamnatinsa za ta gyara dukkan gine-ginen da suka lalace, har da masallacin da ke cikin makarantar.

Haka kuma, ya bada umarni cewa duk wata bukata ta gyaran makaranta a mikata ga Ma’aikatar Ilimi ko ofishinsa domin aiwatarwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda Manoma a Nigeria ke cigaba da kokawa saboda karyewar farashin kayan abinchi

  Farashin kayan abinci kamar masara, gero da shinkafa na...

Inganta ilimi: Jaridar New Telegraph ta Karrama Gwamnan Kano

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Sanarwa ta musamman ga masu neman shiga aikin dansanda

Hukumar kula da aikin 'yan sanda na Kasa (POLICE SERVICE...

Za mu kashe Sama da Naira miliyan 105. Dan Bunkasa Harkar ilimi a karamar hukumar Dala – Hon Surajo Imam

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Surajo...