Karanci ruwa: Manoma a Bagwai sun shiga fargaba

Date:

Daga Shu’aibu Bagwai

 

Manoma a wuraren noma na Madatsar ruwa ta Watari da ke karamar hukumar Bagwai a jihar Kano, sun bayyana fargabar ci gaba da fuskantar mummunar asara sakamakon karancin ruwan noma a gonakinsu fiye da shekaru 3 da suka gabata.

Shugaban Kungiyar Manoman yankin, Alh. Ibrahim Sani Janruwa ya bayyana haka lokacin da yake nunawa manema labarai wuraren da matsalar ta shafa.

Alh. Ibrahim Janruwa ya ce a shekaru 3 da suka gabata Bankin bunkasa harkokin addinin Musulunci na duniya ya bayar da tallafin kudi domin fadadawa da kuma gyara hanyoyin ban ruwa a yankin na Watari amma abun takaici wadanda aka damka al’amarin a hannunsu suka nuna son zuciya da cin amana wajen bayar da aikin ga Dankwangilar da ba Shi da kayan aiki, sakamakon haka ya aiwatar da aiki mara inganci wanda maimakon a sami cigaba sai aka sami koma baya mara adadi.

InShot 20250115 195118875
Talla

Shugaban Kungiyar yace a lokacin yarjejeniyar aikin an cimma matsayar cewar cikin watanni 6 Dankwangilar zai kammala aikin amma sai da ya kwashe fiye da shekaru 3 bai kammala ba, kuma zai rika karbar shawara daga manoman amma suka yi biris da ka’idojin yarjejeniyar saboda suna son su yi aiki mara inganci.

Yanzu-yanzu: Gwamna Yusuf ya nada sabon sakataren gwamnatin jihar Kano

Ya ce sakamakon wannan matsala yanzu haka a kalla gonaki fiye da dubu 10 ba sa samun ruwan amfani wanda hakan babbar barazana ce ga zaman lafiya da cigaban tattalin arzikin jihar Kano.

Alh. Ibrahim Janruwa ya kara da cewa yanzu haka kiyasi ya tabbatar da cewa kaso daya ne kawai cikin kaso 4 na adadin gonakin manoma ke samun ruwan amfani.

Shugaban Kungiyar Manoman ya bukaci hukumomi da Kungiyoyin da abun ya shafa su duba wannan matsalar domin kaucewa fadawa cikin mummunan karancin abinci da rashin aikin yi a yankin da Jihar Kano da ma Kasa baki daya, bisa la’akari da gudunmowar da Madatsar ruwa ta Watari da ke Bagwai ke bayarwa wajen samar da abinci da ayyukan yi a Kasar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...

Kananan Hukumomin Tarauni Rogo da Doguwa sun zamo koma baya wajen yin rijistar Masu zabe a Kano

Rahotanni sun nuna cewa ya zuwa yanzu kananan hukumomin...