Ba fashi za mu gudanar da zaben kananan hukumomin Kano gobe Asabar. KANSIEC

Date:

Daga Mukhtar Yahya Shehu

 

Shugaban hukumar zaben jihar Kano faefesa Sani Lawal Malunfashi ya ce suna nan Kan bakansu na gudanar da zaben kananan hukumomin jihar Kano a ranar Asabar 26 ga watan oktoba na wannan shekara.

Talla

Farfesa Sani Lawal Malunfashi ya sanar da haka yayin Taron manema Labarai dangane da hukuncin babbar kotun jihar Kano na basu dama su cigaba da shirye-shiryen zaben.

Ya ce a matsayin su na masu bin doka, tun a baya kotu ta ba su dama Kuma a kan haka su ke gudanar da ayyukan hukumar.

Matsayar gwamnatin Kano da martanin APC Kan zaɓen Kananan hukumomi

” Hukuncin wannan babbar kotun jihar Kano ya bai wa hukumar zaben ta jiha damar cigaba da shirye-shiryen zaben tare Kuma da umartar duk hukumomin tsaro da ke jihar su Samar da cikakken tsaro yayin zaben.” In ji farfesa Sani Lawal Malunfashi.

Talla

” Duk da cewa ni ba lauya bane amma na san waccan jam’iyyar adawa bata da hurumim shigar da hukumar kara saboda ba ta cikin jam’iyyu 6 da suka cika sharudan hukumar na shiga zaben.” A cewar farfesa Malunfashi.

Ya ce babu APC a zaɓen ƙananan hukumomi da zai gudana a gobe Asabar.

 

Jam’iyyun da za su kara su ne kamar haka: AA, Accord Party, AAC, NRPM da kuma NNPP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...