Kwankwaso Ya Taya Gwamna Yusuf Murnar Samun Kyautar Kwarzon Ilimi na NUT

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jigo a jam’iyyar NNPP ta kasa, Rabi’u Musa Kwankwaso, ya taya gwamna Abba Kabir Yusuf murnar samun lambar yabo ta NUT Golden Award da kungiyar malamai ta Najeriya NUT ta karrama da ita, bisa gagarumar gudunmawar da ya bayar a fannin ilimi.

A wani sako da ya wallafa a sashin shafin sa na X (Twitter) , Kwankwaso ya yabawa Gwamna Yusuf bisa jajircewarsa na farfado da harkar ilimi a Kano.

Talla

Ya bayyana gwamnan a matsayin mai Kwarzo a fannin ilimi tare da kara masa kwarin gwiwa da ya jajirce wajen ganin ya ci gaba da kawo sauye-sauye a fannin ilimi a Kano.

“Ina taya mai girma Abba Kabir Yusuf murnar karramawar NUT Golden Award bisa nasarorin da ya samu a fannin ilimi,” in ji Kwankwaso.

Da dumi-dumi: Jarumi Adam A Zango ya sami Mukami

Ya kuma bukaci gwamna Yusuf da ya karfafa kudurinsa na cimma manyan manufofinsa na sake fasalin ilimi a jihar.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito an bayar da kyautar ne a yayin bikin ranar malamai ta duniya na 2024, wanda ya gudana a dandalin Eagle Square dake Abuja.

Talla

Kungiyar ta NUT tare da hadin gwiwar ma’aikatar ilimi ta tarayya ne suka shirya taron, taron ya hada malamai da shuwagabannin ilimi daga sassan Najeriya domin karramawa tare da nuna matukar farin ciki da nasarorin da aka samu wajen kawo sauyi a fannin ilimi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...