Da dumi-dumi: Jarumi Adam A Zango ya sami Mukami

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gidan Talabijin na Qausain TV ya nada fitaccen jarumin fina-finan Kannywood kuma mawaki Adam A. Zango a matsayin Darakta Janar na gidan Talabijin.

Shugaban kamfanin Qausain, Alh Nasir Idris ne ya bayyana hakan, a wata sanarwa a ranar Litinin a Abuja, ya bayyana cewa nadin Mista Zango a matsayin Darakta Janar din ya fara aiki nan take.

A cewar sanarwar, an amince da nadin ne yayin wani taron hukumar daraktocin kamfanin.

Dalilai 2 da suka sa Gwamnatin Kwankwasiyya ta ce ta cire Sarki Aminu Bayero – Jafar Sani Bello

Alhaji Idris ya kara da cewa an nada tsohon Gwamnan Soja na Jihar Kano, Kanar Sani Bello (mai ritaya) a matsayin Shugaban Hukumar daraktocin kamfaninm

“Nadin Bello a matsayin Shugaban hukumar daraktocin kamfanin na tsawon shekaru hudu ne, kamar yadda dokar Kamfanoni ta tanada.

Talla

Idris ya ce an nada tsohon ministan sadarwa Farfesa Isa Pantami a matsayin mai sanya idanu kan harkokin shugabannin kamfanin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...