Ranar Malamai 2024: NUT ta karrama Gwamnan Kano bisa kawo sauyi a fannin ilimi

Date:

Kungiyar malamai ta Najeriya (NUT) ta karrama gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano, da lambar yabo ta musamman saboda kwazon da ya nuna wajen gyara fannin ilimi a jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya aikowa kadaura24 a ranar Asabar.

Kungiyar ta baiwa gwamnan kyautar ne a yayin bikin ranar malamai ta duniya ta 2024 a dandalin Eagle Square da ke Abuja, a wani gagarumin taron da aka shirya tare da hadin gwiwar ma’aikatar ilimi ta tarayya.

Taron ya tattaro malamai daga jahohi 36 na Najeriya domin karrama wadanda suka ba da gagarumar gudunmawar a fannin ilimi.

An karrama Gwamna Yusuf da lambar yabo ta NUT Golden Award saboda kokarin da ya yi wajen ganin an ceto fannin ilimi na Kano daga rugujewar saboda rashin kulawa.

Tsohon hadimin Buhari a Kano ya kalubalanci kalaman Kwankwaso akan Peter Obi

A nasa jawabin, shugaban NUT na kasa, Kwamared Titus Ambe, ya bayyana cewa gwamnoni shida ne kawai aka zaba domin karramawa, bisa jajircewarsu wajen a ci gaban ilimi, musamman ta hanyar tallafa wa jin dadin malamai da ci gaba da horar da su.

Yayin taron an bayyana nasarorin da Gwamna Yusuf ya samu, ciki har da yadda gwamnatinsa ta ware kashi 29.9 na kasafin kudin Kano na 2024 ga ilimi da kuma ayyana dokar ta-baci a fannin, wanda ya inganta dukkanin ababen more rayuwa da samar da ingantaccen ilimi a jihar.

Talla

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu wanda sakataren gwamnatin tarayya Sanata George Akume ya wakilta ya yabawa gwamnonin bisa sadaukarwar da suka yi.

Da yake jawabi a madadin wadanda aka karrama guda shida da suka hada da Gwamnonin jihohin Borno, Oyo, Benue, Enugu, da Kebbi, Gwamna Yusuf ya jaddada kudirinsa na kara saka hannun jari a fannin ilimi, domin cigaban al’umma .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...