A 2027 za mu sallami Kwankwaso daga Siyasa – Doguwa

Date:

 

 

Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazaɓar Doguwa/Tudunwada, Alhassan Ado Doguwa, ya mayar da martani kan furucin da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi cewa ’yan Najeriya za su kayar da jam’iyyar APC a zaɓen 2027.

Kwankwaso, a lokacin da yake jawabi a wani taron siyasa a Kano, ya ce ’yan Najeriya, musamman ma ’yan Arewa, sun gaji da APC kuma za su sauya ta a zaɓen 2027.

Talla

Doguwa, ya ce Kwankwaso har yanzu bai farfaɗo daga kayen da ya sha a hannun Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2023 ba.

Ya shawarci Kwankwaso ya daina mafarki ya fara neman mafita game da siyasarsa kafin zaɓen 2027.

“A bayyana yake cewar Kwankwaso bai gama warkewa daga shan kaye da ya yi a 2023 a hannun Shugaba Tinubu ba. Furucinsa na cewa ‘yan Najeriya sun gaji da APC ba komai ba ne face mafarki. Ya kamata ya nemi mafita kafin zaɓen 2027,” in ji Doguwa.

Tsohon hadimin Buhari a Kano ya kalubalanci kalaman Kwankwaso akan Peter Obi

Doguwa, wanda shi ne Shugaban Kwamitin Majalisar Wakilai kan Albarkatun Man Fetur, ya ce kalaman Kwankwaso ba su da ma’ana.

“A wani taron siyasa, Kwankwaso ya yi iƙirarin cewa za a sauya APC a 2027. Lokaci ya yi da zai daina mafarki kuma ya amince cewa lokacinsa a siyasa yana gab da ƙarewa.”

Talla

Doguwa ya ƙara da cewa Tinubu yana aiki tuƙuru wajen gyara tattalin arzikin ƙasar da inganta al’amura.

 

Doguwa ya bayyana cewa ya na da yaƙinin cewa matsalolin da ake fuskanta a ƙasar za su ragu nan ba da jimawa ba, yayin da matakan da shugaban ƙasa ya ɗauka za su fara bayar da sakamako mai kyau.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...