Majalisar na neman sa kafar wando guda da shugaban ƙasa Tinubu

Date:

Daga  Isa Ahmad Getso

Majalisar wakilan Najeriya ta sa kafa ta rushe lambar girman da shugaban kasa Bola Tinubu ya bai wa shugaban ta Tajudeen Abbas na CFR.

Talla

‘Yan majalisar suka bayyana fusatarsu da ba shi lambar wanda suka bayyana ta a matsayin bata dace da girman kujerarsa ba, inda suka bukaci sauya masa da irin wadda aka bai wa shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio ta GCON da kuma babban mai shari’a ta kasa.

Da dumi-dumi: Tinubu zai tafi hutu Burtaniya

Majalisar ta ce babu ban-banci tsakanin Akpabio da Abbas, saboda haka ya dace a bai wa shugaban su irin lambar da aka bai wa Akpabio ta GCON maimakon CFR.

Talla

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito shugaban ƙasa Bola Tinubu ya baiwa wasu mutane lambobin girmamawa na kasa, inda ya baiwa shugaban majalisar wakilai lambar yabo ta CFR, a jawabin da ya yiwa yan Nigeria a ranar cikar kasar Shekaru 64 da samun yancin kai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...