Tinubu ya nada dan Kano a matsayin shugaban hukumar bunkasa arewa maso yammaci

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya mika sunayen mambobin hukumar gudanarwa na hukumar raya yankin Arewa maso yamma (NWDC) ga majalisar dattawa domin tantancewa.

A cikin wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da dabaru Bayo Onanuga ya fitar, ya ce matakin ya biyo bayan rattaba hannun da shugaba Tinubu ya yi na kafa dokar hukumar raya yankin arewa maso yamma a ranar 24 ga watan Yuli, wanda ke nuna muhimmin aiwatar da dokar hukumar.

Talla

A cewar sanarwar Ambasada Haruna Ginsau daga Jigawa shi ne zai shugaban hukumar gudanarwar hakumar

Farfesa Abdullahi Shehu Ma’aji (Kano) kuma shi ne shugaban hukumar

Sabon shugaban hukumar NWDC
Sabon shugaban hukumar Arewa maso yamma

Yayin da Membobin suka hada da Dr. Yahaya Umar Namahe (Sokoto),

Hon. Aminu Suleiman (Kebbi)

Talla

Sen. Tijjani Yahaya Kaura (Zamfara)

Hon. Abdulkadir S. Usman (Kaduna)

Hon. Engr. Muhammad Ali Wudil (Kano)

Shamsu Sule (Katsina) da Nasidi Ali mai wakiltar jihar Jigawa.

Talla

Ana sa ran ‘yan kwamitin da aka nada za su ba da gudummawa tare da nuna ƙwarewa wajen ciyar da hukumar bunkasa yankin Arewa maso Yamma.

Hukumar ta NWDC za ta mayar da hankali wajen samar da gagarumin ci gaba, ta fuskar tattalin arziki, da zamantakewa a yankin Arewa maso yammacin Nigeria

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An dakatar da Shugaba da Sakataren kungiyar APC X Eagle forum

Kwamitin zartarwa na kungiyar APC X Eagle forum ya...

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...