Sanya Haraji mai yawa akan taba sigari ne kadai hanyar magance shan ta – CISLAC

Date:

Daga Abubakar Yakubu

 

Wata kungiya mai zaman kanta dake rajin samar da dokokin da zasu taimaka wajen cigaban al’umma mai suna Civil Society Lagislative Advocacy center (CISLAC) ta bukaci gwamnatocin jihohin Nigeria da yi dokokin da zasu kara yawan harajin da suke karba akan kamfanonin taba sigari domin rage yawan masu shanta don inganta rayuwar al’ummarsu.

” Daga lokacin da aka kara kudin harajin taba sigari dole masu kamfanonin za su kara kudin siyanta, hakan zai sa yawan masu siyanta ya ragu ko ma wasu su daina baki daya”.

Talla

Shugaban kungiyar CISLAC na ƙasa Auwal Ibrahim Musa Rafsan Jani ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da kungiyar ta shiryawa masu zuwa da tsaki a harkar.

Ya ce akwai bukatar masu ruwa da tsaki kan batun musamman wadanda suka hadar da ma’aikatar lafiya, muhalli da ta Kuɗi da su tsara yadda gwamnatocinsu zasu samar da dokar kara kudin haraji ga taba sigari don rage illar da take yiwa al’umma.

Gwamnatin Kano ta ciyo bashin makudan kudade don inganta ruwan sha

” Akwai cututtuka da dama suke kama masu shan taba sigari wadanda kuma suna hallaka mutane, sannan hayakinta yana gurbata muhalli da kuma kashe kudade”. Inji Rafsanajani

Yace bayan gwamnatin tarayya ta yi nata kokarin suma gwamnatocin jihohi suna da gagarumar rawar da zasu taka wajen ganin an rage yawan shan taba sigari saboda illar da take da ita ga rayuwar al’umma da muhalli da kuma tattalin arzikin kasa.

Talla

” Kara kudaden harajin zai rage yawan shan tabar saboda masu kamfanonin zasu kara kudinta, Sannan gwamnati za ta sami kudaden shiga da zata iya yin amfani da su wajen gudanar da aiyukan raya kasa da cigaban al’ummarsu.

Masana daban-daban ne suka gabatar da makaloli a yayin taron da aka gudanar jihar kano dake Arewa maso yammacin Nigeria.

Muhalarta taron dai sun fito ne daga jihohin Kano Jigawa Katsina Bauchi da jihar Gombe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...