Yajin Aiki: ASUU Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 14

Date:

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU), ta bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin kwana 14 don warware matsalolin da ke ci gaba da addabar malaman jami’o’i.

Wannan ya biyo bayan ƙarewar wa’adin kwana 21 da ƙungiyar ta bai wa gwamnatin a baya.

Ƙungiyar na neman a kammala tattaunawa kan yarjejeniyar 2009 tsakanin Gwamnatin Tarayya da ASUU, bisa ga sabuwar yarjejeniyar kwamitin Nimi Briggs na 2021.

Talla

Kazalika, suna buƙatar a biya su albashin da aka riƙe saboda yajin aikin da suka yi na tsawon watanni takwas a 2022.

Shugaban ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, ya bayyana takaicinsa kan rashin jajircewar gwamnati kan warware matsalolinsu.

Rasuwar yan sandan Kano babban rashi ne ga Nigeriya – Sarki Aminu Bayero

A cewarsa, “Saboda haka, ASUU ta yanke shawarar sake bai wa Gwamnatin Tarayya wani wa’adin kwanaki 14, a kan ƙarin kwanaki 21 da aka bayar a baya, wanda zai fara daga ranar Litinin, 23 ga watan Satumba, 2024.

Talla

“Ƙungiyar ba za ta ɗauki alhakin duk wani rikici da zai taso ba idan har gwamnati ta kasa yin amfani da wannan dama da ASUU ta ba ta don daƙile rikicin da ke ƙoƙarin tasowa.”

ASUU na kuma neman a biya malaman da ke aikin wucin gadi, da kuma yi wa sabbin waɗanda aka ɗauka aiki ƙarin albashin da aka riƙe musu saboda tsarin biyan albashin gwamnati (IPPIS).

Talla

Haka kuma, suna buƙatar a biya bashin da suke bi na kuɗin haɗin gwiwa da sauran hakkoki.

Sauran buƙatun sun haɗa da samar da kuɗaɗe don farfado da jami’o’in gwamnati, biyan alawus ɗin da aka musu alƙawari a kasafin kuɗin 2023, dakatar da gina jami’o’i ba bisa ƙa’ida ba.

Ƙungiyar tana kuma so a maye gurbin tsarin IPPIS da tsarin UTAS.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Daga Samira Hassan   Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin nan...

Kwankwaso ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso,...

Neman Ilimin addini dana boko da sana’a ba kishiyoyin juna ba ne – Dr. Aminu Sagagi ga matasan Zango

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malamin addinin musulunci a kano...