Yanzu-yanzu: Kotu ta yanke hukunci a karar nemen tsige Ganduje daga shugabancin APC na ƙasa

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

 

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da karar da ke neman a tsige Abdullahi Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar APC na kasa.

Mai shari’a Inyang Ekwo, a hukuncin da ya yanke, ya yi watsi da karar a kan cewa wadanda suka shigar da karar, kungiyar APC ta Arewa ta Tsakiya, karkashin jagorancin Alhaji Saleh Zazzaga, ba ta da wata hujja kan da’awarsu.

Mai shari’a Ekwo, wanda ya ce ba a gabatar da sahihiyar shaida a gaban kotun ba da ke nuna cewa kungiyar na da rajista da Hukumar Kula da Kamfanoni ta kasa ba wato CAC , sannan ya ce doka bata san da kungiyar ba.

Nasarar APC a zaɓen Edo ta nuna yan Nigeria sun gamsu da salon mulkina -Tinubu

Alkalin ya ci gaba da cewa kungiyar ba ta da hurumin shigar da karar saboda batun da suka gabatar a gaban kotun ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar APC.

Ya ce za a iya nadawa ko tsige shugaban jam’iyyar na kasa ta hanyar babban taronta na kasa.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta A ranar 18 ga watan Satumba ne mai shari’a ya sanya yau litinin a matsayin ranar yanke hukunci kan karar.

Talla

Wanda ya shigar da karar, kungiyar APC ta Arewa-Tsakiya, ta shigar da karar ne domin neman cire Ganduje daga matsayin shugaban jam’iyyar APC saboda shi ba dan shiyyar Arewa ta tsakiya ba ne.

A cikin karar mai lamba FHC/ABJ/CS/599/2024, masu shigar da karar sun bayyana Ganduje da APC da kuma hukumar zabe mai zaman kanta a matsayin wadanda ake kara na daya zuwa na uku.

Masu karar sun bukaci kotun ta hana Ganduje ci gaba da bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar APC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Nan gaba kadan za mu bayyana sunayen masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Najeriya – Babban Hafsan tsaro

Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya ce...

Wasu yan daba sun ajiye Makamansu a Kano

Gwamnatin Jihar Kano Hadin gwaiwa da Rundunar Yansandan Jihar...

Masu Mukamai a gwamnatin Kano ba su da uzurin kin taimakawa yan Kwankwasiyya – Sanusi Bature

Mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin...

Magoya bayan Barr Ibrahim Isa (Matawallen Gwagwarwa) sun aikawa Gwamnan Kano Budaddiyar Wasika

Daga Isa Ahmad Getso Kira don nemawa Barr. Ibrahim Isa...