Daga Isa Ahmad Getso
Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da karar da ke neman a tsige Abdullahi Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar APC na kasa.
Mai shari’a Inyang Ekwo, a hukuncin da ya yanke, ya yi watsi da karar a kan cewa wadanda suka shigar da karar, kungiyar APC ta Arewa ta Tsakiya, karkashin jagorancin Alhaji Saleh Zazzaga, ba ta da wata hujja kan da’awarsu.
Mai shari’a Ekwo, wanda ya ce ba a gabatar da sahihiyar shaida a gaban kotun ba da ke nuna cewa kungiyar na da rajista da Hukumar Kula da Kamfanoni ta kasa ba wato CAC , sannan ya ce doka bata san da kungiyar ba.
Nasarar APC a zaɓen Edo ta nuna yan Nigeria sun gamsu da salon mulkina -Tinubu
Alkalin ya ci gaba da cewa kungiyar ba ta da hurumin shigar da karar saboda batun da suka gabatar a gaban kotun ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar APC.
Ya ce za a iya nadawa ko tsige shugaban jam’iyyar na kasa ta hanyar babban taronta na kasa.
Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta A ranar 18 ga watan Satumba ne mai shari’a ya sanya yau litinin a matsayin ranar yanke hukunci kan karar.

Wanda ya shigar da karar, kungiyar APC ta Arewa-Tsakiya, ta shigar da karar ne domin neman cire Ganduje daga matsayin shugaban jam’iyyar APC saboda shi ba dan shiyyar Arewa ta tsakiya ba ne.
A cikin karar mai lamba FHC/ABJ/CS/599/2024, masu shigar da karar sun bayyana Ganduje da APC da kuma hukumar zabe mai zaman kanta a matsayin wadanda ake kara na daya zuwa na uku.
Masu karar sun bukaci kotun ta hana Ganduje ci gaba da bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar APC.