Zaɓen Edo: Magoya Bayan PDP Sun Fara Zanga-Zanga

Date:

 

Magoya bayan Jam’iyyar PDP, sun fara zanga-zanga yayin da ake dakon sakamakon ƙananan hukumomi biyu da suka rage a Zaɓen Gwamnan Jihar Edo.

Jam’iyyar APC, wadda ita ce babbar jam’iyyar adawa a Edo, tana kan gaba a zaɓen bisa sakamakon da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta bayyana.

Hanya ɗaya tak da za a inganta rayuwar yaran da ke barace-barace a Kano da Arewa – Daga Mustapha Hodi Adamu

Magoya bayan PDP, sun mamaye hedikwatar INEC da ke birnin Benin, don yin zanga-zanga kan sakamakon zaɓen da aka gudanar a ranar Asabar, wanda har yanzu ake ci gaba da ƙirga ƙuri’u.

INEC, ta dakatar da bayyana sakamakon bayan ta bayyana sakamakon ƙananan hukumomi 16 daga cikin 18 da ke jihar.

A halin yanzu, APC ta yi nasara a ƙananan hukumomi 10, yayin da PDP ta yi nasara a ƙananan hukumomi guda shida.

Talla

Ana sa ran INEC za ta sanar da sakamakon sauran ƙananan hukumomi biyu da suka rage a yammacin ranar Lahadi.

Tun da farko daily trust, ta ruwaito yadda APC ta kasance a kan gaba da ƙuri’u 244,549, sai PDP da ƙuri’u 195,954, yayin da jam’iyyar LP ke da ƙuri’u 13,348.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Bam ya fashe a Kano ya hallaka wasu ya kuma jikkata wasu

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin...

Kotu a Kano ta sami wani Tela da laifin takurawa makwabtansa da karar keken dinki

Wata kotu a Kano ta samu wani tela da...

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...