Daga Sani Danbala Gwarzo
Tsohon kwamishinan kasafi da tsatsare a gwamnatin data gabata, Ibrahim Dan Azumi Gwarzo ya ce dawo da Jami’ar Sa’adatu Rimi zuwa kwaleji da gwamnatin Kano ta yi daga koma baya ne ga daliban dake karatu a makarantar da kuma bangaran ilimi baki daya.
Dan Azumi Gwarzo ya ce makarantar ta cika duk wasu sharudda na zama jami’a duba da yadda hukumar kula da jami’o’i ta kasa ta tantance tare da bada shedar fara karatun digiri a makarantar.
Dan Azumi Gwarzo wanda ya taba zama kwamishinan ilimi a zangon farko na mulkin Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da wakilin kadaura24.
Ganduje ya musanta kitsa yadda za’a sake tsige sarki Sunusi II
” Wannan matakin Bai da ce ace gwamnatin da take ikirarin mai ilimi muhimmanci ce ta yanke shi ba, domin ya nuna karara cewa gwamnatin kawai adawar Siyasa take ba maganar cigaban al’ummar jihar Kano ba”.
Ya ce gwamnatin ganduje ta yi duk mai yiwuwa wajen samar da gine-gine da kayan aiki da tallafawa makarantar ta zama jami’a da dalibai zasu rika karatun digiri mai makon samun shaidar koyarwa ta N.C.E.
Tsohon kwamishinan ya ce gwamnatin kano bata shiryawa bangaran ilimin ba domin ba gaske take ba.