Inganta Ilimi: Gwamnan Kano ya rabawa makarantu kujerun Zaman ɗalibai

Date:

 

 

A wani mataki na inganta harkar ilimi, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya raba wa makarantu da ke ƙananan hukumomi 44 na jihar, kujeru da tebura 73,800.

Wannan dai na daga cikin ƙoƙarin gwamnan na inganta harkar ilimi a Kano, bayan ƙaddamar da dokar ta-ɓaci kan Ilimi a baya-bayan nan.

Za mu hada hannu domin inganta kasuwar wayar hannu ta Farm Center -Amb. Jamilu Bala Gama

Yayin ƙaddamar da dokar gwamnan, ya jadadda aniyarsa na ganin kowane yaro a jihar ya samu ingantaccen ilimi.

A yayin bikin rabon kujerun da ya gudana a ranar Juma’a, Gwamna Abba, ya jaddada muhimmancin samar da kayan karatu da za su taimaka wa ɗalibai wajen samun ilimi mai inganci.

Gwamnan, ya ce an ƙera kujerun cikin aminci kuma suna da ƙwari, wanda a cewarsa za su taimaka wa ɗaliban da ke ɗaukar karatu a yanzu da ma waɗanda za su zo daga baya.

Talla

Gwamnan, ya kuma gode wa matasa sama da 11,000, masu sana’ar kafinta da walda, waɗanda suka taka rawa gani wajen kammaluwar aikin.

ya jaddada cewar gwamnatinsa za ta ci gaba da taimakon matasa ta hanyar wajen bunƙasa sana’o’insu da kuma samar musu da aikin yi domin yaƙi da zaman banza.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

NURTW ta Karrama DMD Karota Auwal Aranposu

Hukumar dake lura da zirga-zirgar ababa hawa ta jihar...

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...