Inganta Ilimi: Gwamnan Kano ya rabawa makarantu kujerun Zaman ɗalibai

Date:

 

 

A wani mataki na inganta harkar ilimi, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya raba wa makarantu da ke ƙananan hukumomi 44 na jihar, kujeru da tebura 73,800.

Wannan dai na daga cikin ƙoƙarin gwamnan na inganta harkar ilimi a Kano, bayan ƙaddamar da dokar ta-ɓaci kan Ilimi a baya-bayan nan.

Za mu hada hannu domin inganta kasuwar wayar hannu ta Farm Center -Amb. Jamilu Bala Gama

Yayin ƙaddamar da dokar gwamnan, ya jadadda aniyarsa na ganin kowane yaro a jihar ya samu ingantaccen ilimi.

A yayin bikin rabon kujerun da ya gudana a ranar Juma’a, Gwamna Abba, ya jaddada muhimmancin samar da kayan karatu da za su taimaka wa ɗalibai wajen samun ilimi mai inganci.

Gwamnan, ya ce an ƙera kujerun cikin aminci kuma suna da ƙwari, wanda a cewarsa za su taimaka wa ɗaliban da ke ɗaukar karatu a yanzu da ma waɗanda za su zo daga baya.

Talla

Gwamnan, ya kuma gode wa matasa sama da 11,000, masu sana’ar kafinta da walda, waɗanda suka taka rawa gani wajen kammaluwar aikin.

ya jaddada cewar gwamnatinsa za ta ci gaba da taimakon matasa ta hanyar wajen bunƙasa sana’o’insu da kuma samar musu da aikin yi domin yaƙi da zaman banza.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Fadar shugaban ƙasa ta mayar da martani ga Kalaman Kwankwaso

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta zargin Sanata Rabiu Musa...

Yadda Kwamishina a gwamnatin Kano ya tsayawa wani dilan ƙwaya aka bada belin sa a kotu

  Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Namadi, ya tsaya...

Kwankwaso ya caccaki gwamnatin Tinubu

  Tsohon gwamnan jihar Kano, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso ya...

Yanzu-yanzu: Jam’iyyar APC ta yi Sabon Shugabanta na Kasa

  Ministan Jinkai da ba da Agajin Gaggawa, Farfesa Nentawe...