Inganta Ilimi: Gwamnan Kano ya rabawa makarantu kujerun Zaman ɗalibai

Date:

 

 

A wani mataki na inganta harkar ilimi, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya raba wa makarantu da ke ƙananan hukumomi 44 na jihar, kujeru da tebura 73,800.

Wannan dai na daga cikin ƙoƙarin gwamnan na inganta harkar ilimi a Kano, bayan ƙaddamar da dokar ta-ɓaci kan Ilimi a baya-bayan nan.

Za mu hada hannu domin inganta kasuwar wayar hannu ta Farm Center -Amb. Jamilu Bala Gama

Yayin ƙaddamar da dokar gwamnan, ya jadadda aniyarsa na ganin kowane yaro a jihar ya samu ingantaccen ilimi.

A yayin bikin rabon kujerun da ya gudana a ranar Juma’a, Gwamna Abba, ya jaddada muhimmancin samar da kayan karatu da za su taimaka wa ɗalibai wajen samun ilimi mai inganci.

Gwamnan, ya ce an ƙera kujerun cikin aminci kuma suna da ƙwari, wanda a cewarsa za su taimaka wa ɗaliban da ke ɗaukar karatu a yanzu da ma waɗanda za su zo daga baya.

Talla

Gwamnan, ya kuma gode wa matasa sama da 11,000, masu sana’ar kafinta da walda, waɗanda suka taka rawa gani wajen kammaluwar aikin.

ya jaddada cewar gwamnatinsa za ta ci gaba da taimakon matasa ta hanyar wajen bunƙasa sana’o’insu da kuma samar musu da aikin yi domin yaƙi da zaman banza.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...