Hukumar Shari’a a Kano ta dakatar da ma’aikatan kotu kan badaƙalar filaye

Date:

Hukumar Shari’a ta jihar Kano (JSC) ta ladabtar da wasu Magatakardan Kotunan Musulunci biyu kan badaƙalar filaye.

Kakakin Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Kano, Baba Jibo Ibrahim ya sanar cewa ɗaukar matakin ya zo ne a yayin taron hukumar karo na 75 da aka gudanar a ranar 12 ga watan Satumbar nan da muke ciki.

Ya ce hakan na zuwa ne bayan kwamitin bincike da aka kafa kan ƙorafin da aka yi a kansu ya miƙa rahotonsa.

Dalilin da yasa gwamnatin Kano ta rushe Jami’ar ilimi ta Sa’adatu

Binciken ya gano cewa Jamilu Ibrahim tare da waɗanda suka haɗa baki sun karɓi kuɗaɗe ba bisa ka’ida ba, suka bayar da takardar mallakar fili ta hanyar yaudara, domin siyar da wasu filaye guda biyu.

Hakan ce tasa kwamitin ya ba da shawarar a kori Jamilu Ibrahim daga aiki, amma hukumar shari’a ta dakatar da shi ba tare da biyan albashi ba har sai an kammala shari’ar da yake fuskanta a gaban kotun Majiatare.

Shi kuma Zubairu Sulaiman, wanda magatakardan Babbar Kotun Musulunci ne, an same shi da karɓar Naira miliyan ɗaya ta asusunsa na ƙashin kansa a matsayin la’ada bayan siyar da filayen guda biyu.

Talla

A don haka ne shi ma Hukumar shari’a ta dakatar da shi na tsawon watanni huɗu ba tare da biyan albashi ba, kamar yadda kwamitin binciken ya bayar da shawara.

Hakan ce tasa kwamitin ya ba da shawarar a kori Jamilu Ibrahim daga aiki, amma hukumar shari’a ta dakatar da shi ba tare da biyan albashi ba har sai an kammala shari’ar da yake fuskanta a gaban kotun Majiatare.

Shi kuma Zubairu Sulaiman, wanda magatakardan Babbar Kotun Musulunci ne, an same shi da karɓar Naira miliyan ɗaya ta asusunsa na ƙashin kansa a matsayin la’ada bayan siyar da filayen guda biyu.

Masana sun fara sukar matakin gwamnatin Kano na soke jami’ar ilimi ta Sa’adatu Rimi

A don haka ne shi ma Hukumar shari’a ta dakatar da shi na tsawon watanni huɗu ba tare da biyan albashi ba, kamar yadda kwamitin binciken ya bayar da shawara.

A ƙarshe hukumar ta jaddada aniyarta na tsayawa tsayin daka wajen aiwatar da hukuncin da ya dace, kan duk ma’aikaci da ya aikata ba daidai ba musamman waɗanda aka ɗora wa alhakin gudanar da shari’a, don kare mutunci da riƙon amanar ɓangaren shari’a da ma tabbatar da amincewar jama’a.

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Fadar shugaban ƙasa ta mayar da martani ga Kalaman Kwankwaso

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta zargin Sanata Rabiu Musa...

Yadda Kwamishina a gwamnatin Kano ya tsayawa wani dilan ƙwaya aka bada belin sa a kotu

  Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Namadi, ya tsaya...

Kwankwaso ya caccaki gwamnatin Tinubu

  Tsohon gwamnan jihar Kano, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso ya...

Yanzu-yanzu: Jam’iyyar APC ta yi Sabon Shugabanta na Kasa

  Ministan Jinkai da ba da Agajin Gaggawa, Farfesa Nentawe...