Hukumar Shari’a a Kano ta dakatar da ma’aikatan kotu kan badaƙalar filaye

Date:

Hukumar Shari’a ta jihar Kano (JSC) ta ladabtar da wasu Magatakardan Kotunan Musulunci biyu kan badaƙalar filaye.

Kakakin Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Kano, Baba Jibo Ibrahim ya sanar cewa ɗaukar matakin ya zo ne a yayin taron hukumar karo na 75 da aka gudanar a ranar 12 ga watan Satumbar nan da muke ciki.

Ya ce hakan na zuwa ne bayan kwamitin bincike da aka kafa kan ƙorafin da aka yi a kansu ya miƙa rahotonsa.

Dalilin da yasa gwamnatin Kano ta rushe Jami’ar ilimi ta Sa’adatu

Binciken ya gano cewa Jamilu Ibrahim tare da waɗanda suka haɗa baki sun karɓi kuɗaɗe ba bisa ka’ida ba, suka bayar da takardar mallakar fili ta hanyar yaudara, domin siyar da wasu filaye guda biyu.

Hakan ce tasa kwamitin ya ba da shawarar a kori Jamilu Ibrahim daga aiki, amma hukumar shari’a ta dakatar da shi ba tare da biyan albashi ba har sai an kammala shari’ar da yake fuskanta a gaban kotun Majiatare.

Shi kuma Zubairu Sulaiman, wanda magatakardan Babbar Kotun Musulunci ne, an same shi da karɓar Naira miliyan ɗaya ta asusunsa na ƙashin kansa a matsayin la’ada bayan siyar da filayen guda biyu.

Talla

A don haka ne shi ma Hukumar shari’a ta dakatar da shi na tsawon watanni huɗu ba tare da biyan albashi ba, kamar yadda kwamitin binciken ya bayar da shawara.

Hakan ce tasa kwamitin ya ba da shawarar a kori Jamilu Ibrahim daga aiki, amma hukumar shari’a ta dakatar da shi ba tare da biyan albashi ba har sai an kammala shari’ar da yake fuskanta a gaban kotun Majiatare.

Shi kuma Zubairu Sulaiman, wanda magatakardan Babbar Kotun Musulunci ne, an same shi da karɓar Naira miliyan ɗaya ta asusunsa na ƙashin kansa a matsayin la’ada bayan siyar da filayen guda biyu.

Masana sun fara sukar matakin gwamnatin Kano na soke jami’ar ilimi ta Sa’adatu Rimi

A don haka ne shi ma Hukumar shari’a ta dakatar da shi na tsawon watanni huɗu ba tare da biyan albashi ba, kamar yadda kwamitin binciken ya bayar da shawara.

A ƙarshe hukumar ta jaddada aniyarta na tsayawa tsayin daka wajen aiwatar da hukuncin da ya dace, kan duk ma’aikaci da ya aikata ba daidai ba musamman waɗanda aka ɗora wa alhakin gudanar da shari’a, don kare mutunci da riƙon amanar ɓangaren shari’a da ma tabbatar da amincewar jama’a.

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar cigaban Ilimi da gyaran tarbiya ta unguwar zango ta shirya taron kan tarbiyya da tsaro

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malami a jami'ar Bayero dake...

Gwamnatin Kano ta sanar da Ranar Fara hutun zangon Karatu na 3 ga ɗaliban jihar

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da...

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Daga Samira Hassan   Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin nan...

Kwankwaso ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso,...