Dalilin da yasa gwamnatin Kano ta rushe Jami’ar ilimi ta Sa’adatu

Date:

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya soke Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kumbotso, ya mayar da ita kwalejin ilimi.

Kwamishinan yada labarai na Jihar Kano, Baba Ɗantiye, ya sanar cewa, “Gwamna ya rushe hukumar gudanarwar jami’ar nan take”, ya mayar da ita tsohon matsayinta na Kwalejin Ilimi na Sa’adatu Rimi.

“Ya umarci shugaban rusasshiyar jami’ar da ya mika ragamar jagoranci ga mataimakinsa mafi girman matsayi, daga bisani gwamantin jihar za ta sanar da mataki na gaba.”

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Kano ta ayyana ranar Litinin a matsayin Ranar hutu

Ya bayyana cewar an ɗauki matakin ne bayan samun rahoton kwamitin da gwamnatin ta kafa domin lalubo hanyoyin bunkasa harkokin ilimi da kuma tattaunawa da ƙwararru da sauran masu ruwa da tsaki.

Dalilin rushe Jami’ar Sa’adatu Rimi

A cewarsa, an gano cewa tun da farko akwai illa a ɗaga darajar Kwalejin Ilimi na Sa’adatu Rimi zuwa jami’a, la’akari da “kasancewarta a mashigar garin Kano inda dalibai da dama daga wajen birnin suke karatu.

Talla

“Hakan na haifar da barazanar rasa ƙwarrarrun malamai, bambancin albashi da kuma matsalolin gudanar da ita cikin inganci.

“Sannan Majalisar Zartarwa ta lura cewa jihohi da dama a faɗin Najeriya sun ci gaba da gudanar da kwalejojin iliminsu ba tare da wata matsala ba, ƙarƙashin tsarin bayar da takardun shaidar kwarewar malanta da kuma shaidar digiri, ba tare da kwalejojin sun koma jami’o’i ba.”

Makomar Ɗalibai

A cewarsa, soke matsayin jami’ar “ba zai shafi karatun ɗalibanta ba, kuma kwalejin za ta kasance mai bayar da shaidar kammala karatun digiri.

“Sannan za ta ci gaba da gudanar da darussa a wasu fannonin,” da ba na ilimi ba.

Ana iya tuna cewa tsohuwar gwamnatin Abdullahi Ganduje ce ta daga darajar kwalejin ilimin na Sa’adatu Rimi mallakar gwamnatin jihar zuwa jami’ar ilmi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar cigaban Ilimi da gyaran tarbiya ta unguwar zango ta shirya taron kan tarbiyya da tsaro

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malami a jami'ar Bayero dake...

Gwamnatin Kano ta sanar da Ranar Fara hutun zangon Karatu na 3 ga ɗaliban jihar

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da...

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Daga Samira Hassan   Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin nan...

Kwankwaso ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso,...