Yanzu-yanzu: Gwamnatin Kano ta ayyana ranar Litinin a matsayin Ranar hutu

Date:

Daga Rabi’atu Yunusa Adam

 

Gwamnatin jihar Kano ta ayyana ranar Litinin 23 ga watan Satumba a matsayin ranar hutun takutaha.

A wata sanarwa dauke da sa hannun Abba Danguguwa, babban sakataren ma’aikata na ofishin shugaban ma’aikatan gwamnatin jihar, ya ce an ba da hutun ne domin tunawa da zagayowar ranar sunan manzon Allah Sallallahu alaihi wasallam.

Obasanjo, IBB, Abdulsalami na kokarin ganin Atiku da Obi sun maye gurbin Tinubu a 2027

An dai haifi manzon Allah sallallahu alaihi wasallam a ranar 12 ga Rabi’ul Auwal.

Al’ummar jihar Kano na gudanar da bukukuwan a ranar Takutaha, domin murnar haihuwar Annabi Muhammad Sallahu alaihi wasallam.

Takutaha, wani biki ne na tarihi da aka dade da yi tsawon shekaru aru-aru.

Nigerian Tracker

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...