Yanzu-yanzu: Gwamnatin Kano ta ayyana ranar Litinin a matsayin Ranar hutu

Date:

Daga Rabi’atu Yunusa Adam

 

Gwamnatin jihar Kano ta ayyana ranar Litinin 23 ga watan Satumba a matsayin ranar hutun takutaha.

A wata sanarwa dauke da sa hannun Abba Danguguwa, babban sakataren ma’aikata na ofishin shugaban ma’aikatan gwamnatin jihar, ya ce an ba da hutun ne domin tunawa da zagayowar ranar sunan manzon Allah Sallallahu alaihi wasallam.

Obasanjo, IBB, Abdulsalami na kokarin ganin Atiku da Obi sun maye gurbin Tinubu a 2027

An dai haifi manzon Allah sallallahu alaihi wasallam a ranar 12 ga Rabi’ul Auwal.

Al’ummar jihar Kano na gudanar da bukukuwan a ranar Takutaha, domin murnar haihuwar Annabi Muhammad Sallahu alaihi wasallam.

Takutaha, wani biki ne na tarihi da aka dade da yi tsawon shekaru aru-aru.

Nigerian Tracker

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...