Yanzu-yanzu: Gwamnatin Kano ta dage ranar komawa da makarantu

Date:

Daga Mubina Mahmoud

 

Gwamnatin jihar Kano ta dage ranar da za a koma makarantun firamare da na sakandire domin fara karatun shekarar 2024/2025.

Wata sanarwa da daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi Balarabe Abdullahi Kiru ya sanya wa hannu ta ruwaito kwamishinan ilimi Alhaji Umar Haruna Doguwa yana bayyana cewa an yanke shawarar dage ranar da za a koma makarantar ne saboda wasu dalilai na gaba gaggawa.

Umar Doguwa ya bayyana cewa nan ba da dadewa ba ma’aikatar ilimi ta jihar kano za ta sanar da wata rana da za a komawa makarantun.

Farashin man fetur: NNPC ta baiwa Matatar Ɗangote dama

“Ina so in sanar da dalibai da iyayensu cewa sanarwar da aka bayar tun farko na komawa makarantu a ranakun 8 da 9 ga Satumba, 2024, yanzu an dage ta, saboda wasu dalilai na gaggawa da za su taimaka wajen inganta yanayin koyo da koyar da yaranmu. za a sanar da wata ranar nan gaba kadan, “in ji kwamishinan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...

Da dumi-dumi: Wasu kungiyoyin APC a Kano sun fara kiraye-kirayen Abdullahi Abbas ya sauka daga shugaban jam’iyyar

Daga Hafsat Abdullahi Muhammad Kungiyoyin jam'iyyar APC da suka hadar...

Bayan Amincewar Kasar Saudia , an Sanya Ranar Binne Aminu Dantata a Madina

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid...

Rashin Alhaji Aminu Dantata Babban Rashi ne ga harkokin kasuwanci a Duniya – Salbas

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Babban kamfani a masana'antar mai a...