Gyaran bangaren Lafiya: Gwamna Yusuf zai samar da hukumar kula da masu magungunan gargajiya a Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya samu lambar yabo daga kungiyar kwararrun likitocin magungunan gargajiya ta Najeriya bisa kokarin da yake yi na hada kai da wayar da kan mambobinta sama da 5,000 don tallafawa ayyukan kiwon lafiya na jihar.

Gwamnatin jihar ta zabo tare da tantance masu sana’ar sayar da magungunan gargajiya sama da 5,000 da aka ba su takardar shaidar yin maganin gargajiya a Kano daga kananan hukumomi 28 na jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24 ranar Alhamis.

Badakalar magunguna: Dan Kwankwaso zai Maka ICPC, EFCC da PCACC a gaban Kotu

Shugaban kungiyar na kasa Alhaji Maikudi ya bayyana irin kyakkyawar alakar da ke tsakanin kungiyar da jihar, inda ya danganta hakan da kokarin Gwamna Yusuf .

Shugaban kungiyar na kasa ya bayyana jin dadinsa a lokacin kaddamar da kwamitin yaki da cututtuka masu yaduwa na jihar Kano, wanda aka gudanar a fadar gwamnatin jihar Kano.

Ya kuma yabawa Gwamnan kan yadda ya farfado da fannin kiwon lafiya da kuma ba da kulawa ta musamman ga masu Sana’ar magungunan gargajiya.

Tinubu ya yi wa Nigeria illar da za a dade ba a gyarata ba – Atiku Abubakar

Ya kuma nuna jin dadinsa da irin tallafin da gwamnati ta ba su, wanda hakan ya baiwa masu aikin likitanci damar gudanar da aiki yadda ya kamata.

Alhaji Maikudi ya kuma bukaci Gwamnan jihar da ya kafa hukumar kula da magungunan gargajiya domin kara shigar da magungunan gargajiya cikin tsarin kiwon lafiya na jihar.

A nasa jawabin Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yaba da gudunmawar da masu magungunan gargajiya ke bayarwa a fannin kiwon lafiya na jihar.

Ya kuma jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta harkokin kiwon lafiya tare da jaddada muhimmancin hadin gwiwa tsakanin ayyukan masu maganin gargajiya da likitocin zamani.

Gwamnan ya bayyana shirye-shiryen tallafawa masu sayar da magungunan gargajiya ta hanyar basu horo na musamman da samar da hadin gwiwa tsakanin su da cibiyoyin kiwon lafiya, da kuma kafa hukumar da zata rika lura da aiyukansu.

Ya yin hakan zai kara inganta aiyukansu ta yadda zasu cigaba da ba da gudunmawa wajen kula da lafiyar al’umma da kuma haɗa su da tsarin kula da lafiya na jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano Ta Kammala Aikin Gina Mayanka ta Naira Biliyan 1.5

Daga Zakaria Adam Jigirya     Gwamnatin jihar Kano ta karkashin Shirin...

An dakatar da Shugaba da Sakataren kungiyar APC X Eagle forum

Kwamitin zartarwa na kungiyar APC X Eagle forum ya...

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...