Farashin Man Fetur A Nigeria: Ɗangote Ya Magantu

Date:

 

Shugabannin da ke kula da matatar man Ɗangote sun yi watsi da rahotannin da ke nuna cewa an ƙayyade farashin man fetur a kan naira 600 kan kowacce lita, inda ta bayyana rahotannin a matsayin jita-jita marar tushe.

A wata sanarwa da babban jami’in kula da harkokin kasuwanci da sadarwa na kamfanonin Dangote, Anthony Chiejina, ya fitar a shafin sada zumunta na X, ya yi tsokaci kan jita-jitar da ake ta yaɗawa da ke cewa matatar ta na tattauna wa da ƙungiyar dillalan man fetur ta ƙasar IPMAN, a kan yadda za a cimma matsaya wajen sayar da man a kan naira 600 kan kowacce lita.

Dalilin da ya sa na fara yiwa yan siyasa bankada – Dan Bello

Kamfanin ya fayyace cewa bai ƙulla wata alaƙa da ƙungiyar ta IPMAN ,ya kuma jaddada cewa duk wani mataki da kamfaninsu ko matatar da ɗauka za a sanar a hukumance.

Abubunwan da aka tattauna tsakanin Tinubu Buhari Jonathan da gwamnonin Nigeria

Sanarwar ta cewa “An jawo hankalinmu kan labarin da jaridar Punch ta wallafaa da ke cewa kamfanin Dangote ya ƙayyade farashin man fetur kan naira 600 kan kowace lita, a jiya Talata, 13 ga watan Agustan 2024.”

“Za mu so mu fayyace cewa ba mu da ta wata alaƙar kasuwanci da IPMAN a yanzu.”

Ya ce “Ba mu taɓa tattaunawa kan farashin man fetur da IPMAN ba kuma ba su da wani hurumin yin magana a madadinmu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...