An Sace muhimman takardun tuhume-tuhumen da ake yi wa Ganduje – Gwamnatin Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Gwamnatin jihar kano ta ce masu zanga-zangar sun sace Muhimman takardun da ake ake tuhumar tsohon gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa da Kuma wasu daga cikin mukarraban gwamnatinsa .

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a watannin bayan gwamnatin jihar kano ta maka Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa a gaban babbar kotun jihar Kano bisa wasu zarge-zarge na almundahanar kudade.

” Wasu makiya jihar kano sun dauki nauyin wasu bata gari da suka fake da zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa da aka yi a Nigeria, inda suka shiga cikin babbar kotun jihar Kano kuma suka sace Muhimman takardun tuhumar da muke yiwa tsohon gwamnan jihar kano da mukarrabansa”.

Gwamna jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan yayin da ya ziyarci harabar babbar kotun jihar dake sakatariyar Audu Bako.

Dalilin da ya sa na fara yiwa yan siyasa bankada – Dan Bello

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24, ya ce gwamnan ya nuna damuwa kan abun da ya faru na lalata dukiyoyi masu tarin yawa a kotun, tare da sace muhimman takardun tuhumar da ake yiwa shugaban jam’iyyar APC na kasa Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

Sanarwar ta ce masu zanga-zangar sun lalata kaya na sama da naira biliyan 1, wadanda suka hadar da kayan Ofisoshi da sauran kayiyakin amfani na Ofishin babbar mai Shari’a ta jihar Kano da harabar kayan kotun.

“Abin takaici ne matuka yadda makiya jihar Kano suka dauki hayar wasu bata gari suka lalata daya daga cikin gine-ginen al’umma mai dimbin tarihi da nufin kawar da zargin cin hanci da rashawa da ake yiwa Shugaban jam’iyyar APC na kasa kuma tsohon gwamnan jihar Dr. Abdullahi Umar Ganduje da iyalansa da mataimaka.”

Zargin karkatar da shinkafa: EFCC ta karɓi korafi kan shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin Kano

Sanarwar ta kara da cewa barayin sun lalata kusan dukkanin sassan babban kotun da suka hada da ofishin Alkalin Alkalan jihar da hasarar sama da naira biliyan daya ta hanyar sace kayan ofis, lalata ofisoshi, kona motoci da sauran kayan aiki masu muhimmanci ga aikin. na Shari’a .

Alhaji Abba Kabir ya yi kira ga matasa a jihar da su daina bari ana amfani da su wajen yin tashe-tashen hankula, sai dai su maida hankali wajen neman sana’o’in hannu domin samun kyakkyawar makoma tare da jaddada cewa gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’ummar Jihar Kano.

Gwamnan ya bada tabbacin cewa Jiduciary a matsayin fata na karshe na talaka dole ne a kiyaye shi ko ta halin kaka, don haka ya ba da umarnin a gaggauta gyara ginin tare da samar da isasshen tsaro domin tabbatar da adalci.

Ya kuma jajantawa babban alkalin kotun, Dije Abdu Aboki da daukacin yan bangaren shari’a kan wannan munmunan lamari .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...