Yan Sanda sun kama Telan da ke dinkawa masu zanga-zanga tutocin ƙasar Rasha

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Rundunar ‘yan sandan Najeriya, a ranar Litinin ta sanar da kama wani Ahmed Tela, inda ta ke zarginsa da dinka tutocin kasar Rasha da wasu masu zanga-zanga ke amfani da su a Kano da wasu jihohin Arewa.

An kuma kama masu zanga-zanga kimanin 30 da ke dauke da tutocin tare da tsare su.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a hedikwatar hukumar ta farin kaya (DSS) a wani taron manema labarai da ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro ya shirya.

Talla
Talla

Kadaura24 ta ruwaito yadda wasu masu zanga-zangar ke fitowa kan manyan titunan Nigeria musamman jihohin Kano Kaduna Bauchi da wasu jihohin Arewacin Nigeria dauke da tutocin kasar Rasha musamman a wanna rana ta 5 da fara Zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a Nigeria.

Wannan shi ne Ahmad Tela wanda ake zargi da dinka tutar Rasha a Nigeria

An ga masu zanga-zangar dauke da tutocin kasar Rasha suna zagaya tituna suna rera wakoki daban-daban tare da wasu dauke da alluna.

Zanga-zanga: Bayan gurfanar da mutane 632, Gwamnan kano ya magantu kan masu daga tutar Rasha

Daily trust ta rawaito da yake jawabi a wajen taron, Adejobi ya ce daga tutocin wasu kasashe a Najeriya, wadda aka kasa ce mai cin gashin kanta, laifi ne, inda ya kara da cewa wadanda aka kama da wadanda suka dauki nauyinsu za a tuhume su kamar yadda dokar kasar ta tanada kan laifukan da suka aikata.

“Da safiyar yau ne muka kama wani ‘Ahmed Tela’ daga karamar hukumar Nasarawa a jihar Kano, bisa laifin samar da tutocin kasar Rasha masu yawan gaske da ake baiwa matasan Najeriya domin su dagawa.

“ Mun kama shi, Kuma muna kara farautar wasu musamman wadanda suka sa ka su. Kamar yadda nake magana da ku, haka abin ya faru a Kaduna. mun sami damar kama 30 daga cikinsu dauke da tutocin Rasha ” in ji babban jami’in ‘yan sandan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...