Mun bai wa jihohi fiye da naira biliyan 570 don tallafa wa talakawa- Tinubu

Date:

 

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce gwamnatin tarayya ta bai wa jihohin ƙasar 36 fiye da naira biliyan 570 domin faɗaɗa shirye-shiryen tallafa wa talakawansu.

Hakan na ƙunshin cikin jawabin da shugaban ƙasar ya yi da sanyin safiyar yau Lahadi.

Ko a kwanakin baya ma gwamnatin tarayyar ta ce ta bai wa kowace jiha tirela 20 ta shinkafa domin raba wa talakawan ƙasar, kodayake a baya-bayan nan wasu jihohin sun ce ba su samu kasonsu ba.

Talla
Talla

Haka kuma shugaba Tinubu ya ce masu ƙananan sana’o’i 600,000 ne suka samu tallafin bashi daga gwamnatin tarayyar.

Ya ƙara da cewa yanzu haka gwamnati na tantance masu matsakaitan sana’o’i mutum 75,000 domin samun bashin naira miliyan guda kowanennsu, da za su fara samu cikin wannan wata.

Atiku ya yi Allah-wadai da harbin masu zanga-zanga a Kano, Abuja, ya kai karar Tinubu UN da ICC

”Su kuwa masu manyan kamfanoni za mu ba su bashin naira biliyan ɗaya kowannesu don bunƙasa kasuwancinsu”, in ji shugaban ƙasar.

A ranar 1 ga watan Agusta ne dai wasu ‘yan ƙasar suka fantsama kan titunan ƙasar domin gudanar da zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa da suke fuskanta a ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...