Tinubu ya dauki matakin da zai kawo karshen dambarwar Matatar Ɗangote da gwamnatin tarayya

Date:

Daga Umar Usman

 

Majalisar zartaswa ta tarayyar Nigeria a ranar Litinin din nan ta umurci kamfanin man fetur na kasa (NNPC) da ya sayar da danyen mai ga matatar Dangote da sauran matatun cikin gida da kudin kasar nan naira ba dalar Amurka ba.

Shugaban hukumar tattara kudaden haraji ta tarayya (FIRS) Zack Adedeji ya bayyana haka bayan taron FEC da shugaban kasa Bola Tinubu ya jagoranta a Abuja ranar Litinin.

Talla
Talla

Adedeji ya ce matakin zai rage radadin kudaden da kasar ke kashewa a kasashen waje tare da daidaita farashin man fetur da dizal da sauran kayayyakin da ake amfani da su a Najeriya.

Rushe Masarautu: Dan Majalisar Tarayya na NNPP Ya Soki Gwamnatin Kano

Adedeji ya ce majalisar zartarwar ta ba da umarnin cewa ba tare da bata lokaci ba hukumar NNPCPL ta fara aiwatar da wannan umarni don bunkasa masana’antun man fetir na gida Najeriya.

Shugaban hukumar tattara kudaden shigar ya kuma ce gwamnatin Tinubu ta bayar da umarnin matatar Ɗangote ita ma ta sayar da tataccen man ga yan kasuwar mai na gida da naira ba dalar Amurka ba.

Solacebase

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...

Mun gano yadda yan Bauchi ke mamaye dazukan Kano – Gwamnatin Kano

Daga Nazifi Dukawa     Gwamnatin jihar Kano ta ce ta gano...

Gwamnatin Kano Ta Kammala Aikin Gina Mayanka ta Naira Biliyan 1.5

Daga Zakaria Adam Jigirya     Gwamnatin jihar Kano ta karkashin Shirin...

An dakatar da Shugaba da Sakataren kungiyar APC X Eagle forum

Kwamitin zartarwa na kungiyar APC X Eagle forum ya...