Yara Sama da 500 da ba mu san daga inda suke ba na kwana a tashar yankaba dake Kano – Jami’an sa kai

Date:

Daga Ibrahim Sani Gama

 

Shugaban Kungiyar yan kasuwa ta AMATA da ke tashar Yankaba ta jaddada aniyarta na dakatar da masu rashin ayyukan yi a cikin Tashar domin dakile shaye-shayen mugwan Kwayoyi a tashar.

Shugaban kungiyar Nasiru Muhammad ne ya jaddada hakan a lokacin da Kungiyar ta yaye wasu Matasa da suka ajiye Makamansu daga harkokin shaye-shaye.

Nasiru Muhammad ya ce bai kamata a rika tsangwamayar yaran da suke aikata laifuka marasa kyau bai, inda yace yin haka yana taka muhimmiyar rawa wajen kara lalacewarsu.

Talla
Talla

Shugaban Kungiyar ya yi kira gwamnatoci da masu hannu da shuni da su rika zakulo irin wadannan masu aikata laifuka domin neman musu ayyukan yi da su dauke hankulansu da aikata munanan dabi’un da suke aikatawa.

Kungiyar Kwadago Ta Bayyana Matsayarta Kan Zanga-zangar Tsadar Rayuwa a Nigeria

A jawabinsa shugaban jami’an sa kai na tashar yankaba Alh. Bala Danyalwa ya ce akwai wani kalubalen da ya kamata gwamnatin karamar hukuma da ta jiha su magance shi, shi ne magance yawon yara Barkatai a tituna da tashoshin mota.

Ya ce akwai yara kusan Dari biyar da su ke kwana a cikin Tashar yankaba wadanda ba’a san daga inda suka fito ba, wanda barazana ga al’umma.

Talla

Yace, suna iya kokarinsu wajen mayar da wasu da suka San garuruwan iyayensu da jihohinsu Wanda sun mayar da yara da ba za su kirgu ba zuwa jihohinsu Wanda suna yi ne da aljihunsu.

Ya kuma bayyana cewa, nan gaba kadan Kungiyar za ta sake zakulo wasu Matasan da basu da ayyukan yi tare da basu horo akan sana’oi daban daban da ma basu jari.

Wani daga cikin Matasan da suka amfana da wannan tagomashi Muhammad Auwal sani ya godewa Shugabancin Kungiyar ta AMATA Yankaba, bisa jarin da aka bashi tare da Kayayyakin Wankin Mota domin ya dogara da Kawunansu.

Matashin Auwal sani, ya sha Alwashin yin amfani da Kudaden ta hanyar da suka kamata domin dogaro da kansa kamar yadda aka bukacesu,inda ya bayyana cewa, sun yi mutukar farin ciki tare da yin alkawarin ba za su sake aikata Munanan Dabi’u ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...