Kotu Ta Zauna Kan Shari’ar Kwankwaso Da EFCC

Date:

Hukumar Yaƙi da Yi wa Tattalin Arziƙi Ta’annati (EFCC) ta kasa gabatar da takardu a gaban Babbar Kotun Jihar Kano, wanda hakan ya kawo jinkiri a sauraron shari’ar tsakanin hukumar a da jagoran Jami’yyar NNPP na Kasa, Rabiu Musa Kwankwaso da wasu mutum bakwai.

Masu shigar da ƙarar sun haɗa da NNPP, Dokta Ajuji Ahmed, Dipo Olayanku, Ahmed Balewa, Cif Clement Anele, Lady Folshade Aliu, Injiniya Buba Galadima da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Talla
Talla

EFCC ce wadda ake ƙara a wannan shari’ar.

Tsadar Rayuwa: Yadda Wani Malamin Addinin Musulunci Ya Tallafawa Dalibansa

Lauya masu ƙara, Robert Hon, ya ce a shirye suke domin ci gaba da shari’ar.

Ya nuna cewa EFCC na da kwana biyar don shirya wa shari’ar, amma fiye da kwana 30 ta wuce ba tare da sun shirya ba.

Hon, ya bayyana cewa wannan shari’ar ta shafi ‘yancin ɗan adam ne, inda kuma ya roƙi kotu ta yi watsi da buƙatar EFCC na jinkirta shari’ar ba saboda ba su bayar da ƙwaƙƙwaran dalili.

Talla

Lauyan EFCC, Idris Ibrahim Haruna, ya nemi kotun ta ƙara musu lokaci domin su shirya amsarsu.

Alƙalin kotun, Mai shari’a Yusuf Ubale Muhammad, ya ɗage shari’ar zuwa ranar 24 ga watan Oktoba, 2024, domin ci gaba da sauraron ƙarar.

Daily Trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...