Rikicin Masarautun Kano: Yadda Matasa suka hana wakilin Sarki Sanusi shiga gidan sarkin Rano

Date:

Daga Mubina Mahmoud

 

Mazauna Masarautar Rano a ranar Talata sun kori wani mutum da maimartaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya nada domin tafiyar da harkokin masarautar da aka soke har zuwa lokacin da za a yanke hukunci a kotu kan rikicin masarautun a jihar.

Wakilin ya isa garin ne da safiyar ranar Talatar nan, tare da rakiyar manyan masu rike da mukaman siyasa daga yankin, ciki har da babban mataimaki na musamman ga gwamna kan harkokin makarantu masu zaman kansu, Ibrahim Yaluwa, da kuma shugaban karamar hukumar ta Rano, Dahiru Yakubu.

Sai dai wasu fusatattun matasan garin sun rika jifan ‘yan tawagar jim kadan bayan da jami’an karamar hukumar suka kafa tanti a gaban fadar Sarkin Rano da aka kafa domin wakilin ya samu mubaya’a daga dagatai da masu unguwanni.

Talla

A ranar Larabar nan ne wani mazaunin garin Sabiu Ibrahim ya shaida wa manema labarai cewa an tilasta wa tawagar komawa sakatariyar karamar hukumar da ke karkashin kulawar ‘yan sanda.

“Ya shigo garin ne ta karamar hukumar Kibiya maimakon babban titin Kano,” in ji Ibrahim

Mun Rufe Wurin Sallar Da Aka Mayar Da Shi Gidan Gala a Wudil – Bilkisu Indabo

“Sun garzaya zuwa sakatariyar karamar hukumar, inda ya zauna na dan lokaci kafin DPO na ‘yan sanda su fito da shi.”

‘Matasan sun lalata Mota kirar Prado SUV ta wakilin Ranon, Mannir Abubakar, wanda sarki Sanusi II ya tura.

Wani mazaunin garin Garba Rano, ya Matasan sun kuma lalata ababen hawa na yan jam’iyyar NNPP a karamar hukumar.

Kotu ta sanya ranar da Ganduje da Matarsa zasu bayyana a gabanta

Majiyar kadaura24 ta Premium Times ta ce duk kokarin da ta yi na neman kakakin rundunar ‘yan sandan Kano Abdullahi Kiyawa yaci tura.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito majalisar dokokin jihar kano ta soke dokar masarautun Kano ta shekara ta 2019.

Soke dokar na nufin rusa masarautun da aka kirkiro a 2019 – Bichi, Rano, Gaya, da Karaye .

Daya daga cikin sarakunan da aka tsige, Aminu Ado-Bayero na Kano, na kalubalantar tsige shi a gaban kotu, inda ya koma gidan sarki na Nassarawa GRA.

Premium Times

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Tarayya ta Kaddamar da Aikin samar da wutar sola na Naira Biliyan 12 a asibitin Malam Aminu Kano

Kwana biyu bayan rikicin wutar lantarki tsakanin Asibitin Koyarwa...

Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar...

Kungiyar Karamci United Family ta Karrama Shugaban gidan Radiyon Pyramid Saboda Taimakawa Al’umma

Shugaban gidan Radio tarayya Pyramid FM Dr. Garba Ubale...

Kotu ta yanke hukunci kan ko ICPC tana da ikon gudanar da binciken kudin tallafin karatu na Kano

Babbar Kotun tarayya dake Babban Birnin Tarayya (FCT), karkashin...