Kotun Koli Ta Haramta Wa Gwamnoni Taba Kudaden Kananan Hukumomi

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Kotun Koli ta Najeriya ta haramta wa gwamnoni rikewa da kuma gudanar da kudaden kananan hukumomin jihohinsu.

Mai Shari’a Emmanuel Agim na Kotun Koli ya kuma ba da umarnin tura wa kananan hukumomi kudadensu kai-tsaye daga asusun Gwamnatin Tarayya.

Talla

Ya bayyana cewa ce rike kudaden kananan hukumomi da aka tura daga asusun tarayya da gwamnatocin jihohi suke yi ya saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya.

Rikicin Masarautun Kano: Yadda Matasa suka hana wakilin Sarki Sanusi shiga gidan sarkin Rano

Da yake sanar da hukuncin a ranar Alhamis, Mai Shari’a Emmanuel Agim, ya ba da umarnin damka wa kananan hukumomi 774 da ke fadin kasar kudadensu don su ci gaba da gudanarwa.

Alkalin ya kuma kori buƙatar da gwamnatocin jihohi suka shigar na kalubantar neman hana su tasarrufi da kudaden kananan hukumomin.

Ya bayyana cewa a tsawon lokacin da jihohi suka ki ba wa kananan hukumomi ’yancin tafiyar da kudaden, gwamnatocin jihohin ne ke yin gaban kansu da kudaden.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...