Kungiyar Yan Chanji Ta WAPA A Kano Ta Magantu Kan Karyewar Farashin Dala

Date:

Daga Ibrahim Sani Gama

 

Shugaban Kungiyar Masu hada-hadar kudaden canji ta kasashen waje dake jihar Kano, Alhaji Sani Dada ya bayyana jin dadinsa bisa yadda gwamnatin tarayya take kara karya farashin dala kowanne lokaci a kasar.

Kadaura24 ta rawaito Alhaji Sani Dada ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da Manema labarai a ofishinsa dake kasuwar canji ta Wapa, Kano.

Yace rage farashin kudaden waje da babban bankin Kasa yayi, zai fitar da masu hada-hadar canji daga zarge zargen al’umma na cewa sune suke da alhakin tashin gwauran zabin da kayayyakin masarufi suke yi a Kasuwannin Nigeria.

Yanzu-yanzu: CBN Ya Sake Karya Farashin Dala a Nigeria

Shugaban yace wannan kalubale na tsadar kayayyakin masarufi yanzu ya rage tsakanin yan kasuwa da al’ummar Kasar, saboda yanzu jama’a za su fahinci inda gizo yake saka.

” A baya Mutane sun zage mu mun dora mana alhakin tashin Dala Wanda kuma muma bamu da katabus a kai, amma saboda rashin fahimta mutane suka rika Kalubalantar mu har da dora mana alhakin tashin farashin Kayan masarufi”. Inji shi

Halin da Ake Ciki Game da Neman Watan Sallah Karama a Saudiyya

Sani Dada yace kungiyar masu hada hadar canji ta Wapa, ta himmatu wajen ganin an kara inganta rayuwar matasa musamman, ‘ya’yan Kungiyar masu hada hadar canji domin rage marasa ayyukan yi da kuma farfado da tattalin arzikin Najeriya.

Daga karshe Shugaban ya bayyana cewa, Kungiyarsa a shirye take wajen baiwa Gwamnati cikakken hadin kai domin ciyar da jihar Kano da ma Kasa baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda Manoma a Nigeria ke cigaba da kokawa saboda karyewar farashin kayan abinchi

  Farashin kayan abinci kamar masara, gero da shinkafa na...

Inganta ilimi: Jaridar New Telegraph ta Karrama Gwamnan Kano

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Sanarwa ta musamman ga masu neman shiga aikin dansanda

Hukumar kula da aikin 'yan sanda na Kasa (POLICE SERVICE...

Za mu kashe Sama da Naira miliyan 105. Dan Bunkasa Harkar ilimi a karamar hukumar Dala – Hon Surajo Imam

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Surajo...