Da dumi-dumi: Fadar Sarkin Musulmi tace ba a ga watan karamar Sallah a Nigeria ba

Date:

Daga Hafsat Lawan Sheka

 

Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ta tabbatar da cewa ba a sami ganin jinjirin watan Shawwal ba wato watan karamar Sallah a Nigeria.

KADAURA24 ta ruwaito hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa Sakataren kwamitin ganin wata na fadar sarkin Musulmi Farfesa Wali Junaidu ta sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai a Sokoto .

Yanzu-yanzu: Ba a ga jinjirin watan Karamar Sallah a Kasar Saudiyya ba, Dalili

Sanarwar ta ce al’ummar musulmin Nigeria zasu Cika Azumi guda 30 a bana, don haka ya bukaci al’ummar musulmi su dauki Azumin gobe talata.

Sanarwar tace Laraba 10 ga watan afirilu 2024 shi ne ita ce zata Kasance 1 ga watan Shawwal 1445.

Sarkin Musulmi ya kuma yi addu’ar Allah ya karɓi ibadu da addu’o’in da al’ummar musulmi Nigeria suka yi a cikin wannan wata na Ramadan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda Manoma a Nigeria ke cigaba da kokawa saboda karyewar farashin kayan abinchi

  Farashin kayan abinci kamar masara, gero da shinkafa na...

Inganta ilimi: Jaridar New Telegraph ta Karrama Gwamnan Kano

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Sanarwa ta musamman ga masu neman shiga aikin dansanda

Hukumar kula da aikin 'yan sanda na Kasa (POLICE SERVICE...

Za mu kashe Sama da Naira miliyan 105. Dan Bunkasa Harkar ilimi a karamar hukumar Dala – Hon Surajo Imam

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Surajo...