Ciyarwar Azumi: Gwamnan Jigawa ya dakatar da kwamishina a jihar

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Gwamnan jihar jigawa Malam Umar A Namadi, ya dakatar da kwamishinan ma’aikatar Kasuwanci ta jihar Alhaji Aminu Kanta daga mukaminsa har zuwa lokacin da za’a kammala gudanar da bincike kan shirin ciyarwar buda baki a karamar hukumar Babura.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim.

Sanarwar ta ce matakin wani bangare ne na kudirin gwamnati na tabbatar da bin diddigin kudi da kuma tafiyar da kudaden gwamnati yadda ya dace.

Ganduje ya yi martani kan gwamnatin Kano bisa gurfanar da shi a gaban Kotu

Ya ce an dakatar da Kwamishinan ne bisa zarginsa da hannu wajen karkatar da kudaden ciyarwar buda baki a karamar hukumar Babura.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na Ofishin Sakataren gwamnatin jihar Ismail Ibrahim Dutse ya fitar, yace dakatarwar ta fara aiki ne nan take tare .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sabon Rikici Ya Kunno Kai Cikin Jam’iyyar APC a Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Karamin Ministan gidajen da raya burane...

Yadda Manoma a Nigeria ke cigaba da kokawa saboda karyewar farashin kayan abinchi

  Farashin kayan abinci kamar masara, gero da shinkafa na...

Inganta ilimi: Jaridar New Telegraph ta Karrama Gwamnan Kano

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Sanarwa ta musamman ga masu neman shiga aikin dansanda

Hukumar kula da aikin 'yan sanda na Kasa (POLICE SERVICE...