Shahararren Mawakin Hip Hop Ya Karɓi Musulunci A Amurka

Date:

Fitaccen mawaƙi kuma furodusa, Jonathan H. Smith wanda aka fi sani da Lil Jon, ya karɓi addinin Musulunci a wani masallacin garin Culver da ke Jihar California a kasar Amurka.

Kafofin watsa labarai irinsu Daily Sabah da HipHopDx sun ruwaito cewa, a ranar Juma’a Lil Jon ya ziyarci masallacin Sarki Fahad da ke birnin Los Angeles inda ya bayyana cewa ya musulunta a gaban babban taron jama’a.

Gwamnatin tarayya ta bayyana adadin likitocin dake duba lafiyar yan Nigeria sama da miliyan 200

Wani faifan bidiyo da aka yada a shafukan sada zumunta ya nuna mawakin yana karanta shahada da larabci sannan da turanci, karkashin jagorancin limamin masallacin.

Tinubu ya sauke Sha’aban Sharada daga mukamin da Buhari ya bashi, tare da maye gurbinsa da dan Kano

Lil Jon wanda aka haifa a shekarar 1972 a garin Atlanta na Jihar Jojiya, shahararren mawaƙin rap ne saboda rawar da ya taka a matsayin jagaba wajen haɓaka rukunin hip-hop a farkon shekarun 2000.

Lil Jon wanda ke da mabiya fiye da miliyan 1 a dandalan sada zumunta, a baya bayan nan ya sake daukar hankalin jama’a bayan fitowar kundin wakokinsa mai suna Meditation .

Bayan marubuci Ba’amurke kuma mai fafutuka Shaun King, Lil Jon ya zama shahararren Ba’amurke na biyu da ya karɓi Musulunci a makon farko na watan Ramadan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...