Ramadan: Gwamnatin Yobe ta Rage Lokacin aiki ga ma’aikatan gwamnati

Date:

Daga Samira Hassan

 

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya amince da rage sa’o’in aikin gwamnati saboda shigowar watan Ramadan.

Amincewar na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban jami’in yada labarai na ofishin shugaban ma’aikata na jihar Alhassan Sule Mamudo ya fitar kuma ya rabawa manema labarai.

Kotu ta yanke hukunci kan batun nada kantomomi da gwamnan kano yayi

Sanarwar ta ce, a yanzu ma’aikatan gwamnati za su fara aiki ne daga karfe 8:00 na safe zuwa 3:00 na rana, tun daga Litinin zuwa Alhamis, yayin da a ranar Juma’a kuma lokacin aikin ya fara daga karfe 8:00 na safe zuwa 12:00 na rana.

Sanarwar tace wannan rage lokacin ya shafi watan Ramadan ne kawai kuma za’a koma yadda aka saba bayan watan Ramadan,” in ji Sanarwar

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: An zabi sabon shugaban jami’ar Bayero BUK

Daga Rahama Umar kwaru   Farfesa Haruna Musa ya zama sabon...

An sake sauya lokacin jana’izzar Aminu Ɗantata – Gwamnatin Nigeria

Gwamnatin tarayyar Nigeria ta ce Hukumomi a Kasar Saudiyyar...

Fadan daba: ku fito ku Kare Kan ku da iyayenku – Gwamnatin Kano ga matasa

Ku tashi ku Kare kanku da iyayen Gwamnatin jihar kano...