Yadda Mace ta Farko da Gwamnan Kano Ya Baiwa Kantoma Ta Sha Alwashi

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Mace ta biyu da ta rike shugabancin karamar hukuma a Kano Hajiya Bilkisu Yakubu Indabo, ta yi alkawarin fitar da matan jihar kano kunya ta hanyar gudanar da aiyukan da zasu inganta rayuwar al’ummar da take jagoranta.

Hajiya Bilkisu Yakubu Indabo, ita ce mace daya da gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf ya nada ta a matsayin shugabar riko ta karamar hukumar Wudil dake jihar.

A zantawarta da manema labarai Bilkisu Yakubu tace ta San akwai kalubale a gabanta a matsayin ta mace ta farko kuma mace guda da aka nada matsayin shugabar riko ta karamar hukumar, sai dai tace ta shirya sosai domin tunkarar wannan kalubale.

Abin da masu amfani da soshiyal midiya za su ƙaurace wa lokacin azumi

” Tabbatas abun da Maza zasu yi Mata ba zasu iya ba, Amma izinin Allah subhanahu wata’ala zan wannan kallabin da ke tsakanin rawuna zai Bada mamaki, domin nayi Shirin na musamman domin ganin ban baiwa mata kunya ba”.

Buhari ya bukaci yan Nigeria su cigaba da hakuri da manufofin gwamnatin Tinubu

Tace zata tsaya tsayin daka domin gudanar da aiyukan raya kasa da cigaban al’ummar karamar hukumar Wudil, inda tace zata fi mai da hankali wajen inganta harkokin ilimi domin da Ilimi ne za’a iya samun nagartacciyar al’umma wadda za’a yi alfahari da ita.

” Kwankwaso ne ya dauki nayin karatu na tun daga Digiri na farko har zuwa na uku kuma ilimin da nayi shi ya bani damar zawa wannan matakin, don haka nima zan dabbaka wannan sunnar ta jagoranmu Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso don Gina al’ummar karamar hukumar Wudil”.

“Ba zan bai wa Kwankwaso da Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf kunya ba, kuma suma mata ba zan basu kunya ba, zan yi abun da zai sa daga kaina mata zasu rika samun manyan mukami a Kano da izinin Allah”. in ji Bilkisu Yakubu Indabo, matashiyar da gwamnan Kano ya nada shugabar karamar hukumar Wudil ta riko

 

Rahotanni dai sun tabbatar da cewa Hajiya Bilkisu Yakubu Indabo ita ce mace ta biyu da aka taba baiwa rokin kantoma a jihar kano, Inda mace ta farko Fatima Muhammad aka bata kantoma a karamar hukumar Nasarawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnan Kano ya Naɗa Ahmed Musa a Matsayin Janar Manaja na Kano Pillars

Daga Zakaria Adam Jigirya   Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Yanzu:yanzu: Gwamnan kano ya yi sabbin nade-naden mukamai

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Gwamann jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Daga Isa Ahmad Getso   Al'umma da Malaman makaranta a unguwar...

Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar...