Tinubu ya Baiwa Kwastam Sabon Umarni kan yan kasuwar da aka kwacewa kayan abinchi

Date:

Shugaban Kwastam na Kasa, Bashir Adewale Adeniyi, ya ce hukumar za ta mayar wa ’yan kasuwan da ta kwace abincin da suka shigo da shi kayan nasu.

Adeniyi ya ce Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ne ya ba da umarnin domin ba wa ’yan kasuwa damar shigar da kayan nasu da kuma sayarwa a kasuwanni.

Sai dai ya ce sharadin mayar wa ’yan kasuwan kayan abincin shi ne za su sayar wa ’yan Najeriya ba boyewa za su yi ba.

Yadda za ku kula da kanku a lokacin azumin Ramadan

Adeniyi ya sanar da haka ne a taron masu ruwa da tsaki a yankin Kwangwalam da ke kan iyakar Najeriya da Nijar, a Karamar Hukumar Maiadua ta Jihar Katsina ranar Asabar.

A cewarsa, shugaban kasa ya yi haka ne a kokarinsa na ganin ’yan Najeriya sun samu isasshen abincin saya, wanda a cewarsa zai kawo saukin farashi a kasuwanni.

Ku Fara Duban Watan Ramadan Ranar Lahadi – Sarkin Musulmi Ga Musulmi

“A halin yanzu a hannunmu akwai kayan abinci cikin manyan motoci sama da 120 da muka kwace.

“Muna fata idan aka sake su suka shiga kasuwanni a samu sauki.

“Makasudin hakan shi ne samar da tsaro da wadatuwar abinci ga al’ummar Najeriya musamman a wannan hali da ake ciki,” in ji shugaban kwastam din.

A ranar Asabar din shugaban kwastam din ya ziyarci tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari a gidansa da ke Daura, da kuma fadar Sarkin Daura, Dr Umar Farouq Umar, inda aka ba shi sarautar Mabudin Hausa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu:yanzu: Gwamnan kano ya yi sabbin nade-naden mukamai

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Gwamann jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Daga Isa Ahmad Getso   Al'umma da Malaman makaranta a unguwar...

Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar...

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Daga Fatima Mahmoud Diso   Shugabanni da jagororin jam'iyyar APC na...