Yanzu-yanzu: Sheikh Daurawa ya Amince Zai Koma Bakin Aikinsa

Date:

Daga Zainab Abdulhamid

 

Kwamandan Hisbah ta jihar kano Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya dawo mukaminsa bayan sulhun da kungiyar Inuwar hadin kan malaman Kano suka jagoranta tsakanin sa da gwamnan jihar kano.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a ranar Juma’a Sheikh Daurawa ya bayyana Ajiye mukamin nasa bayan wasu kalamai da gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya yi na Kalubalanci yadda hukumar take gudanar da wasu daga cikin aiyukan ta.

Da yake zantawa da Manema labarai Mai magana da yawun gwamnan jihar kano Sanusi Bature Dawakin Tofa yace an sami mahimtar junan ne a wani zama na kimanin tsahon awa guda da akai tsakanin zauren malaman kano da Sheikh Daurawa da kuma gwamna Abba Kabir Yusuf.

Ramadan: Sarkin Kano ya bukaci ‘yan kasuwa da su rage farashin kayan abinci

” Bayan doguwar tattaunawa duk da ba iya abun da ya faru aka tattauna ba , amma dai an sami daidaito domin Malam yace komai ya wuce kuma zai koma aikin sa ma a gobe talata, domin cigaba da aiyukan da ya saba”. Inji Sanusi Bature

Yace “dama tun da farko a wajen gwamnati Malam bai ajiye aikinsa ba, saboda bai rubuta ba , don haka Ina tabbatar maka da cewa an sami masalaha kuma malam zai cigaba da yin aikinsa yadda ya kama.

Muhimmiyar Sanarwa Daga Rundunar Yan Sandan Jihar Kano

A wani rubutaccen jawabi da ya wallafa a sashin shafinsa na Facebook Sheikh Malam Aminu Daurawa ya tabbatar da yin sulhu a dare wannan rana ta litinin.

“ALHAMDU LILLAH
AN SAMI YIN SULHU, ƘARƘASHIN JAGORANCIN INUWAR HAƊIN KAN MALAMAI DA ƘUNGIYOYI,
PROFESSOR BARODO
SHAIK ABDULWAHAB
PROFESSOR SALISU SHEHU
PROFESSOR BABANGIDA
PROFESSOR SA’IDU DUKAWA.
DR MUAZZAM KHALID BUK
DR ENGR BASHIR HANAN
SHAIKH SHEHU MAI HULA
SUKA WAKILCI SAURAN MALAMAI,
ALLAH YA SAKA MUSU DA ALKHAIRI”

“والصلح خير

HISBAH ZA TA CI GABA DA AIKIN TA DARAM BA SANI BA SABO, TARE DA KIYAYE DOKA”. A cewar Daurawa

Wannan batu dai shi ne ya kawo dambarwar da aka kwashe kusan kwana uku zuwa hudu ana yi, wadda ake zargin duk hakan ta farune sakamakon Kamawa tare da gurfanar da Murja Kunya da hukumar Hisbah ta yi a gaban kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...

Da dumi-dumi: Wasu kungiyoyin APC a Kano sun fara kiraye-kirayen Abdullahi Abbas ya sauka daga shugaban jam’iyyar

Daga Hafsat Abdullahi Muhammad Kungiyoyin jam'iyyar APC da suka hadar...