Ramadan: Abdulaziz Yari Zai Raba Tirela 358 na Kayan Abinchi a Zamfara

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Sanata Abdulaziz Yari, mai wakiltar Jhar Zamfara ta yamma, na shirin raba tirela 358 na kayan abinci iri-iri daban-daban.

Kayayyakin da za a raba sun hada da; shinkafa da gero da suga da masara.

Shugaban Kwamitin Yada Labarai na Kungiyar Siyasa ta A Yari, Ibrahim Muhammed, ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Gusau a ranar Lahadi.

Addu’a ce kaɗai maganin rashin tsaro a ƙasar nan – Sanata Abdulaziz Yari

Ya ce za a raba kayan abincin da aka ne don taimakawa mutane wajen gudanar da azumin watan Ramadana ga kowa da kowa ba tare da la’akari da bambancin ra’ayin siyasa ba.

A cewarsa, an shirya tsarin rabon a karkashin kungiyar siyasa ta A Yari bisa jagorancin Lawal Limana wanda ake sa ran magidanta 17,500 za su ci gajiyar rabon.

Muhammad ya bayar da tabbacin cewa kananan hukumomi 13 cikin 14 na jihar za su ci gajiyar shirin.

Gwamnatin Tarayya ta bayyana nasarori data samu sakamakon cire tallafin man fetur a Nigeria

Ya bayyana cewa sama da kashi 98 cikin 100 na kayayyakin tuni an yi nasarar jigilarsu zuwa kananan hukumomi daban-daban na jihar, wanda hakan ya sa wadanda za su ci gajiyar tallafin za su samu nasu kason kan lokaci.

Shugaban kwamitin yada labaran ya bayyana wadanda za su ci gajiyar tallafin, wadanda suka hada da; mabukata da marayu da zawarawa da sauransu.

Muhammad ya tabbatar da cewa za a fara rabon kayan abincin kafin watan Ramadan, ya kuma bukaci jama’a da su yi wa tsohon gwamnan da jihar da kuma kasa baki daya addu’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...