Gudunmawar da Bashir Gentile Ya Baiwa Pyramid Radio Zata Inganta Aiyukan mu – Gm Abba Bashir

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Hukumar gudanarwar gidan Radio tarayya Pyramid fm dake kano ta yabawa shahararren dan Siyasar nan kuma mai fashin bakin kan harkokin siyasar Alhaji Bashir Hayatu Gentile bisa futulu masu amfani da hasken rana guda 5 da bayar aka Sanya domin haskaka harabar gidan Radio.

” Baba shakka wannan abu da Bashir Gentile ya yi mana zai taimakawa ma’aikatan mu su gudanar da aikin su cikin nutsuwa, sannan zai inganta tsaron gidan Radio da kuma kawata gidan radio”.

Hakikanin Yadda Siyasar Kano Zata Kasance a 2027 – Daga Bashir Hayatu Gentile

Shugaban gidan Radio Pyramid Malam Abba Bashir ne ya yi yabon jim kadan bayan kammala aikin sanya futulun masu amfani da hasken rana, wadanda aka sanya su a harabar gidan Radio, jiya Asabar.

Yadda Gwamnan Kano ya baiwa wata mata hakuri bayan bugar Motar ta da ayarinsa sukai

” Babu shakka Mun amfana da zaman da muke da Bashir Gentile a matsayin abokin gidan Radio Pyramid, don haka muna yaba masa matuka, duk da dama ba yanzu ya fara ba, don ko a Shekarar da ta wuce sai da yayi kokarin yin mana rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana, amma abun bai yiwuwa saboda yanayi inga muke akwai duwatsu masu girma”. Inji Abba Bashir

Yadda Pyramid Radio ta koma da daddare

Shugaban gidan Radio Pyramid ya kuma yi kira ga yan siyasa da masu rike da mukaman gwamnati da masu hannu da shuni da su yi koyi da abun alkhairin da Bashir Gentile wajen tallafawa ma’aikatun gwamnati don inganta aiyukan su.

” Wannan gidan na Pyramid Radio na gwamnatin tarayya ne, amma kuma na yan jihar kano ne , saboda kowacce jiha a Nigeria anyi mata nata, don haka akwai bukatar al’umma su rika zuwa suna bamu gudunnawa saboda bafi yawan ma’aikatan gidan Radio yan asalin jihar kano ne”. A cewar shugaban gidan Radio

Malam Abba Bashir ya ce zasu cigaba da kyautata dangantaka tsakanin gidan Radio Pyramid da kuma sauran al’ummar jihar kano don Cika sharuddan da suka sanya aka samar da gidan Radio, na daga darajar al’umma da hada kan kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

INEC ta yi Allah-wadai da masu yakin neman zabe tun kafin lokaci ya yi

Hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC) ta yi Allah wadai...

Yin rijistar katin Zabe zata taimaki addinin musulunci da musulmai – Mal Usman Mai Dubun Isa

Shahararren mai yabon Manzon Allah (S A W) Malam...

Tinubu y ba da umarnin sake Karya farashin kayan Abinci a Nigeria

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bai wa wani...

Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Kulla Alaka Don Inganta Kwarewar Turanci da Samar da Damar Karatu Ga Dalibai A Duniya

  Gamayyar rukunin jami’o’in MAAUN ta kulla yarjejeniyar hadin gwiwar...