Wani Mawaki a Kano ya Maka BBC Hausa a Kotu

Date:

Kotun Tarayya da ke zamanta a Kano ta dage sauraron shari’ar da wani matashin mawaki, Abdul Kamal, ya maka BBC Hausa kan amfani da sautin wakarsa a matsayin taken shirin ‘Daga Bakin Mai Ita’ ba tare da izininsa ba.

A yayin zaman kotun na ranar Litinin, Sashen Hausa na BBC ya nemi kotun ta yi watsi da bukatar mawakin mai suna Abdul Kamal, na biyan s wasu kudi a matsayin diyya daga kamfanin.

Yadda Mota ta Take Wani Mai Kwace Waya da Makami a Kano – Yan sanda

Lauyan BBC, Barista Shakiruddedn Mosobalage, ya bayyana cewa tun da masu kara sun bayyana kudin da suke nema a matsayin tarar amfani da abin da suke kara, to babu bukatar kotu ta bayar da wata oda a kan hakan.

Abdul Kamal ya maka BBC Hausa a gaban kotun ne kan yin amfani da wani sautin kidansa a matsayin taken shahararen shirinsu na ‘Daga Bakin Mai ita’ ba tare da izininsa ba.

Yadda Gobara ta Hallaka Miji da Mata da Yaƴansu 5 a Kano

Lauyansa, Barista Bashir Ibrahim Umar, ya bayyana cewa rokonsu na kan daidai kuma kotu ba ta hurumin yanke wa mutum abin da zai nema a matsayin diyya.

“Idan mai kara ya kai kara dole ne zai fada wa kotu abin da yake so ta yi masa, ba wai ita kotun ce za ta ce ga abin da za a yi wa mai kara ba.”

Alkalin kotun, Mai Shari’a N.M Yunusa, ya dage zaman zuwa ranar 12 ga watan Fabrairu, 2024 don ci gaba da shari’ar.

 

Aminiya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...