Tinubu ya kafa kwamiti domin rage kuɗin iskar gas a Nigeria

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Gwamnatin Najeriya ta bayyana damuwarta kan tsadar iskar gas a ƙasar, kuma ta kafa wani kwamiti da zai yi kokarin lalubo hanyoyin rage farashin gas nan da mako guda tare da magance matsalolin samar da shi a fadin kasar.

Karamin Ministan Albarkatun Man Fetur, Ekperikpe Ekpo ne ya yi wannan tsokaci a kan kalubalen da ke tattare da samar da man fetur da kuma farashin iskar gas a kasuwannin cikin gida.

Talla

Jaridar Daily Trust ta ambato Ekperikpe Ekpo na cewa matakin ya zama wajibi saboda ci gaba da karuwar farashi da iskar gas ke yi a watannin baya-bayan nan, inda ya kai sama da N900 a kan duk kilogiram daya, har ma ya haura N1,200 a wasu jihohin.

Zargin bata sunan APC: Abdullahi Abbas zai maka kwamishinan Abba Gida-gida a kotu

Ministan a cikin wata sanarwa, ya ce manyan kalubalen da aka gano da ke da haddasa karuwar farashin iskar gas sun hada da karancin samun canji kuɗaɗen waje domin sayo iskar gas da kuma ƙarancin kawo gas din kasuwanni Najeriya.

Ministan wanda ya bayyana cewa Najeriya na da arzikin iskar gas, ya ce yanayin da wasu kamfanoni na ƙasashen duniya suka fi damuwa da fitar da iskar gas ba tare da sadaukar da wani adadi mai yawa ga kasuwannin cikin gida ba, abu ne da ba za a amince da shi ba.

Bayan haka ministan ya kafa kwamitin karkashin jagorancin shugaban Hukumar Kula da Harkokin Albarkatun Man Fetur ta Kasa ta Najeriya NMDPRA tare da ba da umarnin fitar da shawarwari kan yadda za a bunƙasa samarwa da kuma tabbatar da ganin an rage farashin iskar gas cikin mako guda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...