Yan kwadago sun rufe titin zuwa filin jirgin sama na Abuja

Date:

Daga Hafsat Yusuf Sulaiman

 

Rahotanni daga filin jirgin saman Abuja na cewa kungiyoyin kwadago sun rufe titin da ke zuwa filin jirgin saman da safiyar yau, Alhamis.

 

Da safiyar nan ne, mutane suka rika wallafa bidiyo na yadda motoci da masu ababen hawa suka tsaya jingum-jingum a kan titin. A daya daga cikin bidiyon da aka wallafa a shafin X, ana iya ganin wata motar dakon kaya daga nesa an gindaya ta a tsakiyar titi.

Talla

Haka zalika, an jiyo kade-kade na tashi, yayin da ake iya hango wasu mutane sanye da tufafi iri daya a kan motocin da ke nesa.

 

Sakataren tsare-tsare na kungiyar NLC, Kwamared Nasir Kabir ya shaida wa BBC cewa mambobinsu sun rufe titin shiga filin jirgin saman na Abuja da kuma hana duk wani jirgin sama da ke da niyyar tashi zuwa jihar Imo.

Dakile Harin Boko Haram a Kano: Sarkin Gaya ya Gargadi Hakimai, Dagatai da Masu Unguwanni

Haka kuma wata sanarwa da babban sakataren NLC, Kwamared Emmanuel Ugboaja ya fitar ta ce matakin ya hadar da filin jirgin sama na Lagos.

 

Ta kuma ambaci matakin da ‘yan kwadagon ke dauka a dambarwarsu da gwamnatin jihar Imo.

 

A ranar Laraba dai 8 ga watan Nuwamban 2023, kungiyoyin kwadago na NLC da TUC suka fara wani yajin aiki, wanda suka sanar da rufe duk wasu harkokin samar da lantarki da na sufurin jiragen sama a jihar ta Imo.

 

Matakin na zuwa ne kwanaki kalilan bayan zargin da kungiyar NLC ta yi wa gwamnan jihar Hope Uzodinma da hadin bakin ‘yan sanda wajen kama shi tare da dukan sa. ‘Yan kwadagon daga bisani sun nuna hoton shugaban kungiyar NLC, Joe Ajaero da idonsa na dama a kumbure.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...

Ba a ga watan Zulqida a Nigeria ba – Sarkin Musulmi

Daga Unmahani Abdullahi Adakawa   Mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad...

Hukumar Shari’a ta Kano ta Gargadi Alkalai 2, ta kuma dakatar da Magatakarda 2

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Hukumar kula da shari’a ta jihar...

Amarya Aisha Humaira ta aike da sako ga masu kage kan alakarsu da Rarara

  Aisha Humaira, amaryar kuma abokiyar aikin mawaki Dauda Kahutu...