Yanzu-Yanzu: Tinubu Yayi Sabbin Nade-nade a ofishin mataimakin Shugaban kasa

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Shugaban kasar Nigeria Bola Tinubu ya nada Kingsley Stanley Nkwocha, tsohon Manaja kuma Editan Jaridar Leadership, a matsayin Babban Mataimaki na Musamman (SSA) kan Harkokin Yada Labarai da Sadarwa a Fadar Shugaban Kasa.

 

Kadaura24 ta rawaito An nada Nkwocha ne tare da wasu da dama da za su yi aiki a ofishin mataimakin shugaban kasa.

Talla

Tinubu ya kuma nada Tope Fasua, babban jami’in gudanarwa na Global Analytics Consulting, a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tattalin arziki a ofishin mataimakin Shugaban kasa .

Da dumi-dumi: Kotu ta yanke hukunci kan zaɓen gwamnan jihar Zamfara

A cikin jerin sunayen, wasu da aka nada a ofishin mataimakin shugaban kasar sun hada da Sadiq S Jambo a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tattalin arziki, Dr. Muhammad Bulama, a matsayin babban mataimaki na musamman kan aiyuka na musamman, Mahmud Muhammad a matsayin mataimaki na musamman na cikin gida, da Ahmed Ningi a matsayin babban mataimaki na musamman kan kafafen yada labarai na zamani da bada agajin gaggawa.

Sauran su ne Stanley Nkwocha mataimakin na musamman kan harkokin yada labarai a ofishin mataimakin Shugaban kasa, sai Tope Kolade Fasua, Mashawarci na Musamman Tattalin Arziki da Sadiq S Jambo Mai baiwa mataimakin Shugaban kasa Shawara kan harkokin tattalin arziki.

Gimba Kakanda, marubuci kuma manazarci kan harkokin jama’a, Tinubu ya nada shi a matsayin Babban Mataimaki na Musamman, kan harkokin Bincike da fashin baki a ofishin mataimakin Shugaban kasa.

Sai Dr. Hakeem Baba Ahmad a matsayin Mai baiwa mataimakin Shugaban kasa Shawara kan harkokin siyasa da Kuma Dr. Aliyu Moddibo mai baiwa mataimakin Shugaban kasa Shawara kan dukkanin al’amura.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...